Sadio Mane ya bada hakuri kan rashin zuwansa Senegal

Asalin hoton, Getty Images
Dan wasan kwallon kafar nan na Liverpool kuma dan asalin kasar Senegal Sadio Mane ya bada hakuri kan rashin kai ziyara kasarsa ta asali bayan ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon kafa na Afirka da hukumar CAF ta ba shi.
Dan kwallon mai shekaru 27 ya karbi kyautar ne a kasar Masar a ranar Talata kuma gaba daya duk an Laraba za tafi Senegal domin nuna murna.
Tuni aka hada mashi kwarya-kwaryan taro a wani gidan tarihi a Dakar babban birnin Senegal.
Sai dai kungiyar kwallon kafa ta Liverpool ta bayyana cewa ''an samu tsaiko da ya fi karfinsa da kuma kungiyar '' wanda hakan ya sa bai je Senegal din ba amma zai je a duk lokacin da ya samu wani sarari.
















