Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labaran abubuwan da ke faruwa dangane da wasanni

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku sharhi da bayanai kan labarin wasannin da zai gudana daga ranar Asabar 24 zuwa 30 ga watan Mayun 2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu da Ahmad Bawage

  1. Zaniolo ya musanta cin zarafin matasan ƴan wasan Roma, Italiya

    Ɗan wasan Fiorentina, Nicolo Zaniolo ya musanta cewa yana da hannu a hatsaniyar da ta ɓarke tsakani da matasan Roma a karawar da Fiorentina ta ci 2-1 a Primavera ta matasa ƴan kasa da shekara 20 a zagayen daf da karshe ranar Litinin.

    A ranar Litinin Roma ta fitar da jawabin cewa Zaniolo yana da hannu cikin rigimar da ta ɓarke - ta kara da cewar har ma doki wasu ƴan wasan.

    Sai dai mai shekara 25, wanda yake buga wasannin aro a Fiorentina daga Galatasaray ya ce ko kusa ba hannunsa a yamutsin.

  2. Brazil ta gabatar da Carlo Ancelotti, Brazil

    Tawagar ƙwallon kafa ta Brazil ta gabatar da Carlo Ancelotti a matakin sabon kociyanta.

    Ɗan kasar Italiya zai kai Brazil zuwa gasar cin kofin duniya da za a buga a Amurka da Mexico da kuma Canada a 2026.

    Tsohon kociyan AC Milan zai yi aikin kan yarjejeniyar zuwa karshen gasar ta cin kofin duniya.

    Ancelotti ya bar Real Madrid a karshen kakar nan, bayan da ƙungiyar Sifaniya ta kasa lashe kofi a kakar nan da yin ta biyu a teburin La Liga a kakar nan.

  3. Ƙungiyoyin da za su wakilci Ingila a gasar Zakarun Turai a 2025/26, Premier League

    A ranar karshe wato Lahadi, Newcastle United ta samu gurbin shiga Champions League a baɗi, duk da rashin nasara 1-0 a hannun Everton a st James Park.

    Newcastle ta kammala kakar nan a mataki na biyar a teburin Premier, bayan da Manchester United ta doke Aston Villa 2-0 a Old Trafford.

  4. Kociyan Newcastle ya ce ba zai sayi ƴan wasa ba, Newcastle United

    Kociyan Newcastle, Eddie Howe ya ce ba zai sayi fitatcen ɗan wasa ba, koda a buɗe kasuwar saye da sayar da ƴan ƙwallo, duk da za su buga Champions League a kakar baɗi.

    A kasuwa uku baya Newcastle ba ta sayo ƴan wasa ba, wadda aka umarta ta sayar da wasu da take da su, domin ta hau kan tsari kashe kuɗi daidai samu ba tare da ta karya ka'ida ba.

    Newcastle United za ta je Champions League, bayan da ta kare a mataki na biyar a teburin Premier League.

    An tambayi Howe ko zai sayo ɗan wasa mai tsada kamar yadda ƙungiyar ta yi 1996, wadda ta ɗauki Alan Shearer kan £15m a lokacin - sai kociyan ya ce ko kusa ba wannan shirin a gabansu.

  5. Salah ya yi kan-kan-kan da tarihin Shearar da Cole, Premier League

    Ɗan wasan Liverpool, Mohamed Salah ya yi kan-kan-kan da Alan Shearer da Andrew Cole a hannu a cin ƙwallaye da yawa a kaka ɗaya a Premier League..

    Salah wanda ya ci Crystal Palace a wasan karshe a babbar gasar tamaula ta Ingila, yana da hannu a cin ƙwallo 47 kenan a bana.

    Ɗan wasan tawagar Masar, ya ci 29, sauran ya bayar aka zura a raga, haka shima Shearer da Cole suka yi a baya a hannun cin ƙwallaye 47 kowanne a kakar tamaula a Premier League.

  6. Man United ta kusan ɗaukar Cunha, Manchester United

    Ana ci gaba da cinikin Matheus Cunha ga Manchester United daga Wolverhampton kan £62.5m.

    BBC ta fahimce cewar an bukaci United ta biya kuɗin sayen ɗan ƙwallo karo uku a kaka biyun da zai rattaba ƙwantiragi a Old Trafford.

    Ana cewa ƙungiyoyin biyu sun kusan cimma yarjejeniya, inda ake sa ran kammala komai a kwanaki masu zuwa.

    Yarjejeniyar Cunha a Wolves ita ce £62.5m, kenan da zarar United ta amince da farashin babu dogon jawabi tsakanin ƙungiyoyin.

    Wata majiya ta ce ana son United ta kammala biyan kuɗin cinikin nan da karshen 2026-27.

    Za a bukaci United ta fara biyan £20.8m, sannan ta biya wasu daga cikin kuɗin a karshen kakar baɗi, sannan ta kammala biya a 2027.

    Cunha ya buga wasa 92 tun bayan da ya koma taka leda a Wolves, wadda ya fara da wasannin aro daga Atletico Madrid a Janairun 2023, ya ci ƙwallo 33 a ƙungiyar.

  7. Labaran da jaridu je wallafawa kan cinikin ƴan wasa, Daga jaridu

    Mataimakin manaja a Tottenham, Ryan Mason na cikin wadanda ake fatan ganin ya maye gurbin kocin West Brom. (Talksport)

    Leicester City ta cimma yarjejeniya kan ɗan wasan gaba a Faransa mai shekara 18 daga Guinea, Abdoul Karim Traore. (Foot Mercato - in French)

    Arsenal na son ɗan wasan Ghana mai buga tsakiya, Thomas Partey ya ci gaba da zama da ita idan kwantiragin da yake kai ya kare, duk da cewa yana samun tayi daga ƙungiyoyi irinsu, Real Sociedad. (football.london)

    Napoli ta gabatar da tayin albashin fam miliyan 23 kan ɗan wasan Belgium mai shekara 33, Kevin de Bruyne a yarjejeniyar shekara uku, bayan barinsa Manchester City a wannan kaka. (Fabrizio Romano)

  8. Tawagar Sifaniya ta gayyaci Gavi da Isco, Wasan neman shiga kofin duniya

    Kociyan Sifaniya, Luis de la Fuente ya gayyaci Gavi da Isco ranar Litinin, domin buga wa kasar karawar daf da karshe a Nations League da za ta fafata da Faransa.

    Rabon da Gavi, mai shekara 20 ya buga wa Sifaniya tamaula tun Nuwambar 2023, sakamakon raunin da ya yi jinya, wanda ya yi wa Sifaniya karawa 27..

    Gavi, wanda ya lashe La Liga da Copa del Rey da Spanish Super Cup a Barcelona, ya buga wasa 42 a kakar nan.

    Wannan shi ne karon farko da Isco zai koma buga wa Sifaniya tamaula tun bayan kaka shida.

    Mai shekara 33, ya samu goron gayyatar sakamakon rawar da ya taka a bana Real Betis da cin ƙwallo12 da bayar da 10 aka zura a raga a wasa 32 da ya buga da ta kai Betis ta samu gurbin Conference League.

    Sifaniya za ta kara da Faransa a Stuttgard ranar 5 ga watan Yuni.

    Ƴan wasan tawagar Sifaniya da aka gayyata Nations League:

    Masu tsaron raga: Unai Simon, David Raya, Alex Remiro

    Masu tsare baya: Pedro Porro, Oscar Mingueza, Robin Le Normand, Pau Cubarsi, Dean Huijsen, Alejandro Grimaldo, Marc Cucurella, Dani Vivian

    Masu buga tsakiya: Martin Zubimendi, Fabian Ruiz, Mikel Merino, Alex Baena, Pedri, Fermin Lopez, Gavi, Isco

    Masu cin ƙwallye: Alvaro Morata, Lamine Yamal, Nico Williams, Yeremy Pino, Dani Olmo, Samu Aghehowa, Mikel Oyarzabal. (Reporting by Pearl Josephine Nazare in Bengaluru, editing by Ed Osmond)

  9. Labaran da jaridu ke wallafawa kan cinikin ƴan ƙwallo

    Daraktan ƙungiyar Napoli Giovanni Manna na shirin ganawa da Manchester United kan yiwuwar cimma yarjejeniya kan ɗan wasan Argentina mai shekara 20, Alejandro Garnacho, wanda ya yi watsi da tayin fam miliyan 40 a watan Janairu daga ƙungiyar ta Italiya. (i paper)

    Arsenal ta bi sahun Bayern Munich a farautar ɗan wasan Brighton mai shekara 28 daga Japan Kaoru Mitoma. (Sky Germany)

    Ɗan wasan gaba a Sweden, Viktor Gyokeres zai yi bankwana da Sporting a wannan kaka. Matashin mai shekara 26 ana alakanta shi da Arsenal da Chelsea kuma akwai yarjejeniyar ba zai bar ƙungiyar da yake ba kan kasa da fam miliyan 84. (Sky Sports)

    Arsenal na son mai tsaron ragar Aston Villa da Argentina, Emiliano Martinez mai shekara 32, domin ya koma ƙungiyar, yayin da ita ma Real Madrid ta kwaɗaitu.(Sun)

  10. Leverkusen ta bai wa Ten Hag aikin kociyanta, Bayern Leverkusen

    Tsohon, wanda ya horar da Manchester United, Erik ten Hag ya saka hannu a kunshin yarjejeniyar kaka biyu a Bayern Leverkusen, ya maye gurbin Xabi Alonso, wanda ya koma horar da Real Madrid.

    Wannan shi ne aikin farko da Ten Hag, mai shekara 55 ya karɓa, tun bayan da United ta kore shi a cikin watan Oktoba.

    Ten Hag ya lashe Carabao Cup da FA Cup a kaka biyu da ya ja ragamar ƙungiyar Old Trafford, sai dai an kore shi a lokacin da United take ta 14 a kasan teburin Premier League.

    Ten Hag ya taka rawar gani a Ajax tsakanin 2018 zuwa 2022 daga nan United ta ɗauke shi.

    Leverkusen karkashin Alonso ta lashe Bundesliga da German Cup a 2023/23 da kai wa zagayen karshe a Europa League.

    To sai ƙungiyar ta kare a mataki na biyu da tazarar maki 13 tsakani da Bayern Munich, wadda ta lashe Bundesliga na kakar nan.

    Ten Hag zai fara aiki daga 1 ga watan Yuli a Bayern Leverkusen.

  11. Netherlands ta gayyaci matashin gola a karon farko, Wasan neman shiga gasar kofin duniya

    Tawagar Netherlands ta gayyaci matashin mai tsaron raga, Kjell Scherpen ranar Litinin, bayan da ta ajiye wanda take amfani da shi, Bart Verbruggen a wasan neman shiga gasar kofin duniya da za ta yi a watan gobe.

    An taɓa gayyatar Scherpen, wanda ya lashe kofin Australia tare da Sturm Graz, domin maye gurbin duk mai tsaron ragar da ya ji rauni, amma bai buga wasa ko ɗaya ba.

    Shi kuwa ɗan wasan Arsenal, Jurrien Timber ba zai buga wa Netherlands karawar ba, sakamakon tiyata da aka yi masa.

    Netherlands za ta buga wasan neman shiga gasar kofin duniya da Finland a Helsinki ranar 7 ga watan Yuni da kuma karɓar bakuncin Malta a Groningen ranar 10 ga watan Yuni.

    Ƴan wasan da Netherlands ta gayyata:

    Masu tsare raga: Mark Flekken (Brentford), Nick Olij (Sparta Rotterdam), Kjell Scherpen (Sturm Graz)

    Masu tsare baya: Nathan Ake (Manchester City), Stefan de Vrij, Denzel Dumfries (both Inter Milan), Jeremie Frimpong (Bayer Leverkusen), Lutsharel Geertruida (RB Leipzig), Jorrel Hato (Ajax Amsterdam), Micky van de Ven (Tottenham Hotspur), Virgil van Dijk (Liverpool), Jan Paul van Hecke (Brighton & Hove Albion)

    Masu buga tsakiya: Ryan Gravenberch (Liverpool), Frenkie de Jong (Barcelona), Justin Kluivert (Bournemouth), Noa Lang (PSV Eindhoven), Tijjani Reijnders (AC Milan), Xavi Simons (RB Leipzig), Mats Wieffer (Brighton & Hove Albion)

    Masu cin ƙwallaye: Memphis Depay (Corinthians), Cody Gakpo (Liverpool), Donyell Malen (Aston Villa), Wout Weghorst (Ajax Amsterdam). (Writing by Mark Gleeson in Cape Town; Editing by Aidan Lewis)

  12. Raya na fatan lashe safar zinare karo na uku a jere, Premier League

    Mai tsaron ragar Arsenal, David Raya na fatan lashe ƙyautar safar zinare a Premier League a baɗi, bayan da ya karɓi ƙyautar bana tare da golan, Nottingham Forest, Matz Sels.

    Kowannesu ya yi wasa 13 ba tare da ƙwallo ya shiga ragarsa ba a kakar nan, waɗanda aka bai wa ƙyautar ranar Lahadi, bayan kammala Premier League ta kakar nan.

    Sai dai an ci Raya a wasan da Arsenal ta je ta doke Southampton 2-1 a St Mary, yayin da Chelsea ta yi nasara cin Forest 1-0 a dai ranar karshen ta Premier League.

    An zura ƙwallo 34 a ragar Raya, yayin da 46 aka ci Forest, kuma Arsenal, wadda ta samu gurbin Champions League, ita take da masu tsare baya da ba su bari ƙwallaye da yawa sun shiga ragarta ba.

    Raya ne ya lashe ƙyautar safar zinare a matakin wanda ya yi wasa da yawa ƙwallo bai shiga ragarsa ba a 2023/24, wanda yake fatan zai ɗauki karo na uku a jere a baɗi.

  13. Da ƙyar idan zan iya kalubalantar Liverpool a baɗi - Guardiola, Premier League

    Pep Guardiola ya ce da wuya idan Manchester City za ta iya komawa kan ganiya ta kalubalanci Liverpool, wajen lashe Premier League a baɗi.

    City za ta je Champions League a kaka mai zuwa karo na 15 a jere, bayan da ta yi nasara 2-0 a gidan Fulham a wasan karshe a Premier League.

    Ƙungiyar ta Etihad wadda ta ci wasa 21 da canjaras takwas da rashin nasara tara ta haɗa maki 71, ta kare a mataki na uku a teburin babbar gasar tamaula ta Ingila.

    Sai dai City ta kammala kakar bana ba tare da cin kofi ba a karon farko bayan kaka takwas, wadda tsakaninta da Liverpool da tazarar maki 13.

    Liverpool ta lashe Premier League na kakar nan na 20 jimilla.

  14. Union Saint-Gilloise ta lashe kofin Belgium bayan kaka 90, Union Saint-Gilloise

    Ranar Lahadi Union Saint-Gilloise ta kawo karshen shekara 90 rabon da ta dauki kofin babbar gasar tamaula ta Belgium.

    Ta yi namijin kokarin doke Gent da cin 3-1, hakan ya sa ta kammala kakar bana a matakin farko da tazarar maki uku tsakani da Club Brugge ta biyu.

    Kungiyar da ke birnin Bruseel ta yi kokarin kaucewa abin da ya faru a bara a wasan karshe da ta kasa daukar kofin na babbar gasar tamaula ta Belgium – tana da na 14 jimilla yanzu haka.

    An kafa kungiyar ranar 1 ga watan Nuwambar 1897, kenan tana da shekara 127.

  15. Xaud ne sabon shugaban hukumar ƙwallon kafar Brazil, Brazil

    An zabi Samir Xaud a matsayin sabon shugaban hukumar kwallon kafar Brazil, bayan da wata kotu a Rio de Janeiro ta kori Ednaldo Rodrigues daga kan mukamin.

    An gudanar da zaben ne, bayan da ake sa ran kaddamar da Carlo Ancelotti a matakin wanda zai ja ragamar tawagar Brazil.

    Xaud wanda shi kaɗai ya yi takarar mukamin ya samu kuria 101 daga 143 da aka kaɗa.

    A farkon makon nan tsohon shugaban ya ce ya janye daukaka karar da ya shigar domin a samu ci gaban kwallon kafar Brazil

  16. Labaran da jaridu ke wallafawa kan cinikin ƴan ƙwallo, Daga jaridu

    Shugaban Napoli, Aurelio de Laurentiis ya tabbatar da cewa su na farautar De Bruyne. (II Mattino, via Mirror)

    Daraktan wasanni a Arsenal, Andrea Berta ya tatauna da ɗan wasan AC Milan, Rafael Leao, mai shekara 25, a kokarin kawo shi Emirates a wannan kaka. (TeamTalk)

    Norwich City ta tuntubi kocin Bristol City, Liam Manning kan yiwuwar daidaitawa da shi a sabuwar kaka. (Telegraph - subscription required)

    Arsenal ta gabatar da tayin saye ɗan wasan nan mai shekara 21 daga RB Leipzig, Benjamin Sesko. (Fichajes - in Spanish)

  17. Real Madrid ta gabatar da Alonso a matkin sabon kociyanta, Real Madrid

    Real Madrid ta gabatar da Xabi Alonso a matakin sabon kociyanta ranar Litinin, wanda ya maye gurbin Carlo Ancelotti, shi kuma dan kasar Italiya zai koma horar da tawagar Brazil.

    Alonso tuni ya amince da kunshin yarjejeniyar da za ta kare a karshen kakar 2028,

    Mai shekara 43 ya fara aikin jan ragamar Bayern Leverkusen a Oktoban 2022 da lashe Bundesliga a karon farko a tarihin kungiyar kuma ba tare da rashin nasara ba a kakar.

    Leverkusen wadda ta dauki German Cup da kai wa wasan karshe a Europa League a bara ta kare a mataki na biyu a Bundesligar bana, za ta je Champions League a badi.

  18. An bai wa Liverpool kofin Premier League na 20 jimilla, Premier League

    An kammala gasar Premier League ta kakar nan ranar Lahadi, inda aka bai wa Liverpoll kofin bana da ta lashe, na 20 jimilla, duk da tashi 1-1 da Crystal Palace a Anfield.

    Wadda take ta biyu Arsenal ta je ta doke Southampton da cin 2-1 a St Mary.

    Manchester City da Chelsea da Newcastle United duk sun samu tikitin buga Champions League a baɗi.

    Chelsea ta ci 1-0 a gidan Nottingham Forest, haka ita kuwa Manchester City ta je ta doke Fulham 2 -0 a Craven Cottage,

    Yayin da Newcastle ta yi rashin nasara 1-0 a hannun Everton, kuma a St James Park..

    Tottenham, kuwa kashi tasha a gida a hannun Brighton da 4-1, inda Manchester United ta yi wa Aston Villa fancalen zuwa Champions League, sakamakon doke ta 2-0 a Old Trafford.

    United, wadda ta yi rashin nasara a hannun Tottenham a Europa League ranar Laraba,ba ta lashe kofi ba a bana, sannan ba za ta je gasar Zakarun Turai ba karon farko tun bayan 2014/15.

  19. Norris ne ya lashe gasar Monaco Grand, Formula One

    A gasar tseren motocin Formula, direban McLaren, Lando Norris ne ya lashe Monaco Grand Prix a ranar Lahadi.

    Charles Leclerc ne na biyu da kuma Oscar Piastri matukin motar McLaren a matsayi na uku.

    Norris shi ne kan gaba a teburi da tazarar maki uku tsakani da Pistri - ana sa ran za a fafata a makon gobe a Barcelona Grand Prix.

  20. French Open ta karrama Rafael Nadal, Ƙwallon tennis

    An karrama Rafael Nadal a French Open a karshen mako, inda abokan hamayyarsa suka mara masa baya da ya hada da Roger Federer da Novak Djokovic da kuma Andy Murray.

    An damkawa Nadal zakara French Open 14 wani kofi na kawa na musamman - dan kasar Sifaniya ya yi ritaya a bara.