Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labaran abubuwan da ke faruwa dangane da wasanni

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku sharhi da bayanai kan labarin wasannin da zai gudana daga ranar Asabar 24 zuwa 30 ga watan Mayun 2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu da Ahmad Bawage

  1. Mataimakin kociyan Liverpool, Heitinga zai karɓi aikin kocin Ajax

    An bai wa mataimakin kociyan Liverpool, John Heitinga izinin ya je ya tattauna da Ajax kai aikin horar da ƙungiyar.

    Ajax ta kasa lashe kofin babbar gasar tamaula ta Netherlands wato Eredivisie ranar karshe, hakan Francesco Farioli ya yi murabus, kaka ɗaya a kan ragama.

    Heitinga, wanda ya koma Anfield tare da Arne Slot kan fara kakar da aka kammala, ya buga wasa a Ajax da horar da karamar ƙungiya da yin aikin kociyan riƙon ƙwarya na wata biyar daga Janairun 2023 daga nan ya koma mataimakin David Moyes a West Ham.

    Liverpool ta amince da mataimakin Slot, mai shekara 41 tsohon ɗan wasan Everton da Fulham da ya je ya tattauna da Ajax kan aikin horar da ita.

  2. Rawar da Barca ta taka wajen lashe kofi uku a kakar 2024/25

    An kammala kakar 2024/25, wadda abin alfahari ce ga Barcelona, sakamakon lashe La Liga da Coapa del Rey da Spanish Super Cup da ta yi.

    Ƙungiyar ta yi namijin ƙwazo a kakar farko da sabon koci, Hansi Flick ya ja ragama, har ya kai ƙungiyar zagayen daf da karshe a Champions League.

    Sai dai ta kasa kai wa karawar ƙarshe a gasar ta zakarun Turai, bayan da Inter Milan ta fitar da ita.

  3. Super Eagles za ta buga wasa da Ghana, Unity Cup

  4. Za a auna koshin lafiyar Zubimendi kafin ya kammala komawa Arsenal, Arsenal

    Ɗan wasan Real Sociedad, Martin Zubimendi za a auna koshin lafiyarsa kafin a kammala cinikinsa zuwa Arsenal.

    Wata majiya mai karfi ta sanar da BBC cewar an cike duk wata takardar da ta shafi batun cinikin ɗan wasan kan komawa Emirates da taka leda, inda kaɗan ya rage a kammala komai.

    Da zarar an kammala auna koshin lafiyar ɗan wasan mai shekara 26 cikin nasara daga nan Arsenal za ta sanar da sayen shi.

    An ce ƙudin sayen ƙunshin yarjejeniyar Zubimendi ya kai £51m, an kuma amince da yadda Arsenal za ta biya Sociedad ƙudin cinikin.

    An daɗe Arsenal tana ta son ɗaukar Zubimendi.

    Da zarar Gunners ta kammala batun ɗaukar Zubimendi, za ta mayar da hankali wajen zawarcin gurbin mai cin ƙwallaye ciki har da Benjamin Sesko da Viktor Gyokeres daga wanda ta tsara za ta nema.

    Haka kuma Arsenal tana tattaunawa kan tsawaita yarjejeniyar Bukayo Saka da William Saliba da Gabriel da Leandro Trossard da Thomas Partey da Myles Lewis-Skelly da kuma Ethan Nwaneri.

  5. Arteta baya kokari a Arsenal - Henry, Arsenal

    Arsenal ba ta kokari a karkashin Mikel Arteta a kaka uku baya da ya ja ragamar ƙungiyar, in ji tsohon ƙyaftin ɗin Gunners, Thierry Henry.

    Arteta, mai shekara 43, ya mayar da Arsenal kan ganiya tun bayan da ya bar aikin mataimakin Pep Guardiola a Manchester City a 2019, inda koda yaushe ake rige-rigen lashe Premier League da ita.

    To sai dai ƙungiyar ta kasa lashe kofi tun bayan FA Cup da ta ɗauka bayan cin Chelsea a wasan karshe a kakar farko ta Arteta a Arsenal a 2020.

    Arsenal tana karewa a mataki na biyu karo uku a Premier League, wadda aka yi waje da ita a Champions League a zagayen daf da karshe da League Cup da FA Cup a kakar nan.

  6. Salah bai san makomarsa ba idan ya gama wasa a Liverpool

    Ɗan wasan Liverpool, Mohamed Salah ya ce bai san makomarsa ba da zarar ya kammala kaka biyun da zai yi nan gaba a Anfield.

    Sai dai ya ce zai ci gaba da taka leda har zuwa ya cika shekara 40 da haihuwa, kuma ƙungiyoyin Saudiyya na ci gaba da tuntuɓarsa.

    A watan jiya ƙyaftin ɗin tawagar Masar ya tsawaita ƙwantiragin kaka biyu, wanda ya ci ƙwallo 29 a bana a Premier League.

    A satumbar 2023 Al Ittihad ta Saudiyya ta taya shi kan farashin £150million, amma ya zaɓi ci gaba da taka leda a Liverpool.

    A kwanaki masu zuwa Salah zai cika shekara 33 da haihuwa.

  7. Enrique ya bukaci ƴan wasan PSG su saka sunansu a tarihin Champions League, Paris St Germain

    Kociyan Paris St Germain, Luis Enrique ya bukaci ƴan wasan ƙungiyar da su saka sunansu a tarihin lashe Champions League a karon farko a tarihi, kofin da take neman tun da dadewa.

    Wadda ta lashe babban kofin tamaula na Faransa na bana za ta fuskanci Inter Milan a Allianz Arena ranar Asabar, duk wadda ta yi nasara ta lashe Champions League.

    Tuni dai PSG ta dauki kofi biyu a bana, wadda take fatan lashe na uku jimilla

  8. Van Dijk na addu'ar samun sauki ga waɗanda suka ji rauni a harin da aka musu, Liverpool

    Ƙyaftin ɗin Liverpool, Virgil van Dijk yana addu'ar samun sauki ga waɗanda mota ta buge bayan da ake bikin lashe Premier League ranar Litinin da yammaci.

    Ƴansandan Merseyside, sun sanar cewar suna tsare da wani mai shekara 53, wanda ake zargi da yunkurin kisa da tukin ganganci kuma cikin barasa.

    Kimanin mutun 50 abin ya rutsa da su, har da wani jariri da ya ji mummunan rauni.

    A ranar Talata an sanar cewar mutum 11 har yanzu na saibiti, bayan tun farko aka kai mutum 50, domin duba lafiyarsu.

  9. Labaran da jaridu ke wallafawa kan cinikin ƴan ƙwallo, Daga jarida

    Manchester City ta zage damtse kan farautar ɗan wasan tsakiya a AC Milan da Netherlands, Tijjani Reijnders, mai shekara 26, wanda aka kiyasta kuɗinsa kan £55m. (Mail)

    Ɗan wasan tsakiya a Brazil, Casemiro mai shekara 33, da na Argentina Alejandro Garnacho, mai shekara 20, na cikin 'yan wasan da Manchester United ke son rabuwa da su a sabon kaka. (Telegraph - subscription required)

    Manchester United ta tattauna da ɗan wasan Brentford da Kamaru, Bryan Mbeumo mai shekara 25, da aka yiwa kuɗi £50m. (Talksport)

    Newcastle United na tattaunawa da ɗan wasan Ingila mai shekara 22, Liam Delap, a kokarin ganin sun shawo kan ɗan wasan na Ipswich ya dawo garesu maimako ya je Everton ko Manchester United ko Chelsea. (TeamTalk)

  10. Mane ba zai buga wa Senegal wasan sada zumunta biyu ba, Wasannin sada zumunta

    Sadio Mane ba zai buga wa Senegal wasan sada zumunta biyu da za ta yi nan gaba ba, wanda ya nemi izinin a barshi ya huta.

    Mane ne daga fitattun da suka saba bugawa Senegal tamuala da ba zai yi karawar ba da aka gayyaci ƴan wasa 26 da koci, Pape Thiaw ya sanar ranar Talata.

    Thiaw ya sanar da manema labarai cewar Mane, mai shekara 33, wanda ya buga wa Senegal karawa 111 ya sha suka da cewar bai yi kokari ba a fafatawa da suka tashi canjaras da Sudan, amma suka doke Togo a karawar neman shiga gasar kofin duniya a cikin watan Maris.

    Koci, Thiaw ya gayyaci Mamadou Lamine Camara a karon farko cikin tawagar, wanda ya taka rawar gani a ƙungiyarsa, Renaissance Berkane ta Morocco, wadda ta lashe African Confederation Cup ranar Lahadi.

    Ɗan wasan Chelsea, Nicolas Jackson da Iliman Ndiaye daga Everton, waɗanda ba su buga wasan cikin watan Maris ba, za su yi wa Senegal wasan biyu na sada zumunta.

    Senegal za ta fara wasa da tawagar Ireland a Dublin ranar 6 ga watan Yuni, sannan ta kece raini da Ingila a Nottingham ranar 10 ga watan Yuni.

    Tawagar Senegal da za ta buga wasan sada zumunta biyu:

    Masu tsare raga: Mory Diaw (Rodez), Yevhann Diouf (Stade Reims), Edouard Mendy (Al Ahli)

    Masu tsare baya: Abdou Diallo (Al Arabi), El Hadj Malick Diouf (Slavia Prague), Ismail Jakobs (Galatasaray), Kalidou Koulibaly (Al Hilal), Antoine Mendy (Nice), Moussa Niakhate (Olympique Lyonnais), Abdoulaye Seck (Maccabi Haifa)

    Masu wasa daga tsakiya: Lamine Camara (Monaco), Mamadou Lamine Camara (Renaissance Berkane), Pathe Ciss (Rayo Vallecano), Habib Diarra (Racing Strasbourg), Krepin Diatta (Monaco), Idrissa Gana Gueye (Everton), Pape Gueye (Villarreal), Pape Matar Sarr (Tottenham Hotspur)

    Masu cin ƙwallye: Boulaye Dia (Lazio), Idrissa Gueye (Metz), Nicolas Jackson (Chelsea), Cherif Ndiaye (Red Star Belgrade), Iliman Ndiaye (Everton), Cheikh Sabaly (Metz), Ismaila Sarr (Crystal Palace), Abdallah Sima (Stade Brest).

  11. Norrie ya yi waje da Medvedev a zagayen farko a French Open, French Open

    Ɗan Burtaniya, Cameron Norrie wanda yake na 81 a jerin waɗanda ke kan gaba a ƙwallon tennis, ya yi waje da tsohon lamba ɗaya, Daniil Medvedev a zagayen farko a French Open ranar Lahadi.

    Medvedev ya yi rashin nasara da ci 7-5, 6-3, 4-6, 1-6, 7-5, kuma karo na shida da aka yi fatali da shi a zagayen farko a gasar da ake yi a birnin Paris..

    Norrie ya kai zagayen gaba cikin kasa da awa hudu, kuma karon farko da ya doke Medvedev a wasa biyar da ya fafata da ɗan kasar Rasha.

    Gasar da Medvedev mai shekara 29 ya taka rawar gani a French Open, ita ce ta 2021 da ya kai kwata fainal.

    Norrie, shima mai shekara 29, ya kai zagaye na biyu a gasar ta birnin Paris karo na biyar, zai kuma fuskanci Aleksandar Kovacevic ko kuma Federico Gomez.

  12. Ya kamata Bruno ya ci gaba da taka leda a Man United - Amorim, Manchester United

    Ruben Amorim ya fayyace mahimmacin Bruno Fernandes a Manchester United, wadda za ta yi shirye-shiryen tunkakar kakar baɗi, bayan da ta kasa taka rawar gani a bana.

    Fernandes, mai shekara 30, yana taka rawar gani a United, wadda ta kare kakar nan a mataki mafi muni tun bayan 1973/74 - hakan ya sa har da Europa League da Tottenham ta lashe bayan cin United 1-0 a makon jiya.

    Rashin nasarar nan ya sa ana ganin watakila, ƙyaftin ɗin United ya bar ƙungiyar.

    Ana alakanta Bruno da Al Hilal ta Saudiyya, bayan da Amorim ya ce Bruno yana da mahimmaci a United.

  13. Zverez ya kai zagaye na biyu a French Open, French Open

    Alexander Zverev ya fara French Open da kafar dana, bayan da ya yi nasara a kan wani matashi, Learner Tien a gasar ta Roland Garros ranar Talata.

    Ɗan kasar Jamus, wanda ya yi rashin nasara a wasan karshe a bara a hannun Carlos Alcaraz a gasar French Open ya yi nasarar cin 6-3, 6-3, 6-4 a karawar da suka yi a filin Suzanne Lenglen.

    Zverev zai buga wasan zagaye na biyu da ko dai Jesper de Jong ko kuma Francesco Passaro.

  14. Mitchell zai bar aikin daraktan wasannin Newcastle, Newcastle United

    Daraktan wasannin Newcastle sporting, Paul Mitchell zai bar aikin kasa da shekara ɗaya a kan mukamin.

    Mitchell, wanda aka ɗauka bayan da Dan Ashworth ya koma Manchester United a Yulin bara, zai bar Newcastle cikin mutunta juna a karshen watan Yuni.

    Ya koma Newcastle, wadda ya yi aiki da takwaransa babban jami'i, Darren Eales, waɗanda suka yi aiki tare a Tottenham, koda yake Eales zai shima zai bar Newcastle, saboda batu na neman lafiya.

  15. Labaran da jarida ke wallafawa kan cinikin ƴan wasa, Daga jarida

    Chelsea ta tattauna da Eintracht Frankfurt kan ɗan wasanta mai shekara 22 daga Faransa, Hugo Ekitike. Hakazalika suna zawarcin ɗan wasan Sweden da ke taka leda a Sporting, Viktor Gyokeres mai shekara 26, da Delap na Ipswich. (Independent)

    Eintracht Frankfurt ta yi wa ɗan wasan da Chelsea ke so Ekitike kudi a kan £84m. (Athletic)

    Ɗan wasan Sunderland mai shekara 19 da ke buga tsakiya, Jobe Bellingham ya je Jamus inda yake tattaunawa da Eintracht Frankfurt - kwana biyu da taimakawa ƙungiyarsa. Borussia Dortmund - inda ɗan wasan Jude ke taka leda - da Leipzig duk sun kwaɗaitu da ɗan wasan. (Sky Sports)

    Manchester United na son ɗan wasan Wolves da Portugal, Nelson Semedo. Ɗan wasan mai shekara 31kwantiragin da ya ke kai zai kare a wannan kakar. (Football Transfers)

  16. Ancelotti ya ce yana murna da ya karɓi aikin horar da Brazil, Brazil

    Sabon kociyan Brazil, Carlo Ancelotti ya ce an martaba shi da aka yi masa tayin aikin horar da kasar, kuma yana alfahari, yana kuma fatan zai lashe kofin duniya a 2026.

    Mai shekara 65 an kaddamar da shi ranar Litinin a hedikwatar hukumar ƙwallon kafar Brazil.

    Ɗan kasar Italiya, wanda ya bar kociyan Real Madrid, ya lashe Champions League uku da La Liga biyu tare da ƙungiyar ta Sifaniya.

    Haka kuma Ancelotti ya ɗauki kofin zakarun Turai biyu a AC Milan da Premier League da FA Cup a Chelsea da babban kofin Faransa da na Jamus, wato Bundesliga.

    Brazil, wadda ta lashe kofin duniya karo biyar na karshe da ta ɗauka shi ne a 2002, inda Ancelotti zai fara jan ragamar wasa biyu na neman shiga gasar kofin duniya daga Kudancin Amurka.

    Brazil za ta kara da Ecuador ranar 5 ga watan Yuni daga nan ta kece raini da Paraguay a Sao Paulo kwana biyar tsakani.

    Ancelotti ya samu tarbar girma a wajen tsohon kociyan Brazil, Luiz Felipe Scolari, ya kuma maye gurbin Doriyal Junior, bayan wasan da Argentina ta casakara Brazil 4-1 a cikin watan Maris.

    Brazil tana ta huɗu a teburin Kudancin Amurka, saura wasa huɗu suka rage, inda shida daga yankin za su je buga gasar kofin duniya kai tsaye da za a yi a Amurka da Mexico da kuma Canada.

    Brazil ta ci karo da koma baya tun daga 2022 da aka fitar da ita a gasar kofin duniya a Qatar a hannun Croatia a bugun fenariti a kwata fainal.

    Tun daga lokacin Brazil ta yi rashin nasara biyar daga wasa 14 da ta yi, sannan aka zura mata ƙwallo 16 a raga.

  17. Man United ba ta bukatar fitattun ƴan wasa - Amorim, Manchester United

    Ruben Amorim ya ce Manchester United ba ta bukatar sayen fitattun ƴan wasa don tunkarar kakar baɗi, bayan da ta kasa samun gurbin shiga gasar zakarun Turai ta baɗi da kasa lashe kofi a kakar nan.

    Ranar Laraba Tottenham ta ci Man United 1-0 ta lashe Europa League a birnin Bilbao a Sifaniya, kuma United ta kare a mataki na 15 a kasan teburin Premier League.

    United tana ziyara a Kuala Lumpur, domin buga wasannin sada zumunta guda biyu da za ta yi.

    Ƙungiyar da Amorim ke jan ragama za ta fara wasa da fitattun Asia ranar Laraba daga nan ta kece raini da tawagar Hong Kong ranar Juma'a.

    United ta je buga wasan sada zumunta da Casemiro da Alejandro Garnacho da kuma Bruno Fernandes.

  18. Labaran da jarida ke wallafawa kan cinikin ƴan wasa, Daga jarida

    Daraktan wasanni a Bayer Leverkusen, Simon Rolfes ya tabbatar da burin Liverpool na mallakar ɗan wasan Jamus mai shekara 22, Florian Wirtz. (Sky Sport Germany - in German)

    Daraktan wasanni a Napoli, Giovanni Manna ya ce suna ta tattaunawa kan cimma yarjejeniya da ɗan wasan tsakiya a Belgium, Kevin de Bruyne, mai shekara 33. A wata mai zuwa kwantiraginsa ke karewa a Manchester City. (Rai News - in Italian)

    Chelsea da Bayern Munich da Manchester United sun kwaɗaitu da ɗan wasan gaba a AC Milan da Portugal, Rafael Leao mai shekara 25, a wannan kaka. (Teamtalk)

    Newcastle na duba yiwuwar tsawaita zaman ɗan wasanta na Ingila mai shekara 33, Callum Wilson. (Athletic - subscription needed)

    Ƙungiyar Ligue 1 Paris FC na son cimma yarjejeniya da dan wasan Senegal mai shekara 35, Idrissa Gueye, wanda kwantiraginsa ke karewa a Everton a watan gobe. (Foot Mercato - in French)

  19. Yadda aka samu ƙungiyoyin da za su buga Champions League a baɗi, Champions League

    A ranar Lahadin da ta gabata ce bayan fama da kwan-gaba-kwan-baya a sakamako, ƙungiyoyin Manchester City da Chelsea da Newcastle suka samu gurbin shiga gasar cin kofin zakarun turai ta baɗi.

    A rannar ce aka kammala gasar kasashen Turai, inda aka samu waɗanda suka samu gurbin shiga Champions League a baɗi.

    Ga jerin waɗanda za su fafata a gasar zakarun Turai a kaka mai zuwa

  20. Al Ittihad ce ta lashe kofin gasar kwallon kafa ta Saudiyya, Saudiyya

    Al Ittihad ce ta lashe kofin babbar gasar tamaula ta Saudiya ranar Litinin, bayan cin Damac 1-0.

    Ƙungiyar da Lauren Blanc ke horarwa ta ɗauki kofin tun saura wasa bibiyu a karkare kakar bana, amma sai a ranar Litinin aka ba ta kofin a gaban magoya bayanta a filin King Abdullah a Jedda, wanda ya ci makil da ƴan kallo.

    Kenan Al Ittihad na fatan lashe kofi na biyu a Saudiyya, wadda za ta kara da Al-Qadisiyah a King's Cup of Champions ranar Juma'a