Babu batun ƴan shidan farko a yanzu a Premier League
Kociyan Arsenal, Mikel Arteta ya ce yanzu ba batun manyan ƙungiya shida a Premier League.
Gunners za ta karɓi bakuncin Newcastle a wasanta na karshe a bana a Emirates ranar Lahadi, kuma dukkansu suna neman gurbin Champions League, Arsenal tana ta biyu da tazarar maki biyu tsakani da ƙungiyar St James Park.
Ƙungiya biyar ake sa ran za ta wakilci Ingila a baɗi a Champions League, sai dai ana sa ran su zama shida, bayan kammala wasan karshe a Europa League tsakanin Tottenham da Manchester United a makon gobe.
Chelsea da Aston Villa da Manchester City, kowacce na neman gurbin gasar zakarun Turai.
Arteta ya ce gasar Premier ta kara tsauri, kuma yadda suka ga sauye-sauye a kakar nan, lallai za a yi tata ɓurza a baɗi sai mai rabo.