Kociyan Newcastle United, Eddie Howe ya ce yana sa ran zai samu gurbin Champions League.
Ranar Lahadi Arsenal ta ci Newcastle 1-0 a wasan mako na 37 a Premier League a Emirates.
Hakan ya sa Gunners ta ci gaba da zama ta biyu a teburin babbar gasar tamaula ta Ingila da maki 71, sannan za ta wakilci Ingila a gasar zakarun Turai a baɗi.
Kenan Liverpool, wadda ta lashe kofin Premier League na bana na 20 jimilla da Arsenal, sune suka samu tikitin shiga Champions League daga Ingila, kenan saura gurbi uku ake nema nan gaba.
Kawo yanzu Newcastle tana ta uku da maki 66, iri ɗaya da na Chelsea ta huɗu da Aston Villa ta biyar, Manchester City mai ƙwantan wasa tana da maki 65 a mataki na shida da kuma Nottingham Forest ta bakwai da maki iri ɗaya da na City.
Ranar Lahadi za a karkare wasannin kakar bana.