Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Arbeloa zai bar aikin kociyan Real Madrid a karshen kakar bana

Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga 17 zuwa 24 ga watan Mayun 2026.

Taƙaitattu

  • Ingila za ta buga gasar kofin duniya ba tare da Foden da Palmer da Arnold
  • Burin Ronaldo ya ci ya lashe babban kofin Saudiyya a bana
  • Manchester United ta tabbatarwa da Carrick mukamin kociyanta
  • Guardiolazai bar Manchester City bayan sama da shekara 10 a Etihad
  • Mourinho na son Rashford a Madrid, Everton na harin Osula
  • Arbeloa zai bar Real Madrid a karshen kakar nan
  • Brazil ta saka Neymar cikin ƴan wasan da za su buga mata kofin duniya
  • Ku shiga zaurenmu na BBC Hausa WhatsApp
  • Za ku iya tafka muhara a shafnmu na sada zumunta a BBC Hausa Facebook

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Arteta ne na biyu da ya buga Premier ya kuma lashe kofin a matakin kociya, Premier League

    A wani rubutu da aka wallafa a Facebook, ƙungiyar Professional Footballers’ Association ta yi ikirarin cewa Mikel Arteta shi ne “dan wasan Premier League na farko da ya taɓa lashe gasar a matsayin koci.”

    Sai dai Arteta shi ne dan wasan Premier League na biyu da ya jagoranci ƙungiya ta lashe kofin Premier League a matsayin koci.

    Tun bayan kafa gasar Premier League fiye da shekara talatin da suka gabata, akwai kociyoyi guda 13 da suka taba lashe kofin gasar.

    Mikel Arteta shi ne mutum na farko da ya ɗauki kofin Premier League a matsayin kocin ƙungiyar da ya taɓa bugawa wasa a cikin gasar.

    Sai dai Roberto Mancini ya riga shi yin hakan, lokacin da ya lashe Premier League a kakar 2011/12 a matsayin kocin Manchester City. Kafin nan, Mancini ya taɓa buga wasa a Premier League lokacin da aka aro shi zuwa Leicester City tsakanin watan Janairu da Fabrairu a shekarar 2001.

    Kocin da ya fi kowa nasara a tarihin Premier League shi ne Sir Alex Ferguson, wanda ya lashe kofin 13 tare da Manchester United tsakanin kakar 1992/93 zuwa 2012/13. Ferguson ya yi duk rayuwar wasansa ne a Scotland, don haka bai taba buga wasa a Ingila ko Premier League ba.

    Pep Guardiola ya lashe Premier League sau shida tare da Manchester City. Ya shafe mafi yawan rayuwar wasansa a Barcelona, kuma bai taba buga wa wata ƙungiyar Ingila tamaula ba.

    Jose Mourinho ya lashe Premier League uku tare da Chelsea. Ya yi gajeriyar rayuwar wasansa gaba daya a Portugal.

    Arsene Wenger ya lashe Premier League uku tare da Arsenal. Shi ma ya yi wasansa ne a Faransa.

    Bayan Arteta da Mancini, sauran kociyoyin da suka taɓa lashe Premier League sun yi hakan sau daya kacal:

    • Carlo Ancelotti, Antonio Conte da Claudio Ranieri – duk sun yi wasansu a Italiya
    • Manuel Pellegrini – ya yi wasa a Chile
    • Jurgen Klopp – ya yi wasa a Jamus
    • Arne Slot – ya yi wasa a Netherlands

    Sir Kenny Dalglish shi ne koci na karshe da ya lashe Premier League a kakar 1994/95. Ya taba buga wasa a matakin koli a Ingila tare da Liverpool, amma ya riga ya yi ritaya kafin fara kakar Premier League ta farko a watan Agustan 1992.

  2. Arsenal ce ta lashe kofin Premier League na bana, Premier League

  3. Arsenal ta lashe Premier League na bana na 2025/26, Premier League

    Jiran shekara 22 da Arsenal ta yi na fatan lashe kofin Premier League ya kawo ƙarshe bayan da abokiyar hamayyarta Manchester City ta tashi kunnen doki da Bournemouth a wasan da ake sa ran zai kasance na biyu kafin na ƙarshe ga Pep Guardiola a matsayin kocin City.

    Sakamakon wasan na ranar Talata ya bar ƙungiyar da Mikel Arteta ke jan ragama da tazarar maki huɗu a saman teburi kafin wasannin ƙarshe na kakar da za a buga ranar Lahadi, inda ake sa ran Gunners za ta ɗaga kofin a wasanta da Crystal Palace.

    Kafin karawar ana ta batu kan rahotannin da ke cewa Guardiola zai sauka daga aikin horas da City a ƙarshen kakar bana.

    Kafin fara wasan, Guardiola ya shaida wa kafafen talabijin cewa rade-radin makomarsa bai shafi shirye-shiryen ƙungiyar “ko kaɗan” ba, amma City ta sha wahala sosai a hannun Bournemouth wadda ke neman gurbin zakarun Turai a baɗi, wadda ta tsawaita wasa 17 a jere ba tare da rashin nasara ba.

    Kocin Bournemouth, Andoni Iraola, ya sanar cewa zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana, kuma wannan sakamakon ya tabbatar da cewa ya taimaka wa ƙungiyar samun gurbin buga gasar Turai a kakar wasa mai zuwa — babban tarihi ga Bournemouth.

  4. An bai wa Maran aikin horar da tawagar Albania, Gasar kofin duniya

    An naɗa Rolando Maran a matsayin sabon kocin Albania kan kwantiragin shekara guda da rabi, kamar yadda hukumar ƙwallon ƙasar ta sanar a ranar Talata.

    Maran, mai shekaru 62, ya maye gurbin ɗan Brazil, Sylvinho, wanda wa’adinsa ya ƙare bayan Albania ta kasa samun tikitin shiga gasar cin kofin duniya wato FIFA World Cup 2026.

    Kocin ɗan kasar Italiya yana da kwarewa a fannin ƙwallon ƙafa a kungiyoyi, inda ya horar da fitattu da suka haɗa da Cagliari Calcio da Genoa da Bari da kuma Brescia Calcio.

    Shugaban hukumar ƙwallon ƙafar Albania, Armand Duka, ya ba Maran aikin kai ƙasar ga nasara a rukuni na UEFA Nations League, da kuma samun tikitin shiga UEFA Euro 2028, tare da kuma kafa burin dogon lokaci na kai Albania gasar FIFA World Cup 2030.

  5. , Daga Jaridu

    Jose Mourinho da ke shirin komawa Real Madird na harin dauko ɗan wasan gaban Ingila Arcus Rashford. da ke taka leda a matsayin ɗan wasan aro a Barcelona daga Manchseter United. (Sport - in Spanish)

    Everton da Auston Villa na son ɗan wasan Newcastle William Osula. (The I)

    Baba wani ci gaba kan batun tsaiwata kwantaragin ɗan wasan bayan Ingila Levi Colwil, da Chealsea, sai dai za a iya komawa terburin tattaunawa a kaka mai zuwa. (Sky Sports)

    Manchester United da Chelsea na son ɗauko ɗan wasan gaban Jamus Karim Adeyemi a wannan kaka, inda Borussia Dortmund ke son siyar da shi kan farashin da ya dace. (Teamtalk)

  6. Martinez ya ce ya yi farar dabara da ya ci gaba da wasa a Aston Villa, Premier League

    Emiliano Martínez ya ce ya yi farar dabara da ya yanke shawarar ci gaba da zama a Aston Villa, bayan da ya kusa barin Villa Park a bara.

    Mai tsaron ragar mai shekara 33, wanda ya lashe FIFA World Cup tare da Argentina a Qatar a 2022 ya kusa barin Villa Park a karshen kakar 2024–25 bayan da ya yi ban kwana cike da hawaye ga magoya baya a wasan karshe da Tottenham Hotspur.

    Yanzu kuma, yana dab da lashe babban kofi a zakarun Turai, yayin da Aston Villa ke shirin buga wasan karshe a UEFA Europa League da Freiburg a birnin Istanbul.

    Martínez ya shiga Aston Villa a watan Satumba 2020, kuma ya sake jaddada soyayyarsa ga kungiyar kafin wannan muhimmin wasan, yana mai cewa zamansa a ƙungiyar ta zama yanke shawara mai kyau.

  7. Carragher ya caccaki Arne Slot kan Salah, Premier League

    Arne Slot ba zai iya samun “nasara” ba, duk yadda ya tafiyar da lamarin Mohamed Salah a wasan ƙarshe a kakar bana, in ji tsohon ɗan wasan Liverpool, Jamie Carragher.

    Carragher ya ce kocin ba shi da isasshen iko da zai iya cire Salah daga wasan karshe ranar Lahadi, saboda matsayin ɗan wasan na tsawon lokaci da tasirinsa a ƙungiyar.

    Salah ya wallafa wani saƙo a shafukansa na sada zumunta a ranar Asabar, wanda aka ce ya yi kama da yabon tsohon kocin Liverpool, Jürgen Klopp, abin da ya ƙara rura wutar rade-radin rashin jituwa tsakaninsa da Slot.

    Ana sa ran Salah zai buga wasan ƙarshe a kakar Premier League da Brentford a ranar Lahadi a Anfield.

    Wasan yana da muhimmanci sosai ga makomar Liverpool a neman gurbin gasar UEFA Champions League, dangane da sakamakon wasu ƙungiyoyi kamar Bournemouth da Manchester City.

    Carragher ya ce duk wani sakamako a wannan wasan zai fi muhimmanci, amma idan hakan bai yi tasiri ba, to zai zama dama ga Slot ya nuna matsayinsa ga ɗan wasan tawagar Masar, wanda ya taka rawar gani a Anfield.

  8. Guardiola bai yi karin bayani a Bournemouth kan barinsa Man City a bana ba, Premier League

    Pep Guardiola ya je filin wasa na Vitality ba tare da ya yi tsokaci kan rahotannin da ke cewa zai bar Manchester City a karshen kakar wasa ta bana ba.

    An ruwaito tun a daren Litinin cewa ana hasashen Guardiola zai sauka daga mukaminsa da zarar ya ja ragamar karawar karshe a Premier League da za ta buga da Aston Villa ranar Lahadi.

    BBC Sport da sauran kafafen yaɗa labarai sun bayyana cewa har yanzu Manchester City ba ta fitar da wata sanarwa ba kan wannan jita-jita, kuma Guardiola ya mai da hankali kan wasan da ke gabansa.

    Tun bayan zuwansa Etihad a 2016, City ta lashe kofuna 20 ciki har da na Premier League shida da UEFA Champions League daya.

    Sun kuma lashe FA Cup sau uku da kuma EFL Cup sau biyar, ciki har da dukkan wadannan kofuna a wannan kakar.

    Haka kuma an ce tsohon mataimakinsa, Enzo Maresca ne ke kan gaba wajen maye gurbinsa, bayan da ya bar aikin horar da Chelsea a farkon wannan shekara.

    Maresca ya taɓa aiki karkashin Guardiola a kakar 2022–23 lokacin da City ta lashe kofi uku Treble, sannan daga baya ya jagoranci Leicester City komawa buga Premier League, inda a Chelsea ya lashe FIFA Club World Cup da UEFA Europa Conference League.

  9. An kori Southampton daga wasan cike gurbi, bayan leken asirin wasu ƙungiyoyi, Southampton

    An kori Southampton daga wasannin cike gurbin shiga Premier League a baɗi daga Championship bayan ta amince da zargin leƙen asirin atisayen wasu ƙungiyoyi uku.

    Middlesbrough — wadda ta sha kashi a hannun Southampton a wasan kusa da na karshe — an mayar da ita cikin gasar, kuma za ta kara da Hull City, domin neman tikitin komawa Premier League.

    Hukumar English Football League ta tuhumi Southampton da leƙen atisayen Oxford United da Ipswich Town, sannan kuma da yin bidiyo a Middlesbrough, yayin shirye-shiryen su kafin wasan farko a daf da karshe a ranar 7 ga watan Mayu.

    Kwamitin ladabtarwa mai zaman kansa ya kuma rage maki huɗu ga Southampton a kakar EFL Championship ta gaba.

    Wannan hukunci ya sa ƙungiyar ta rasa damar buga wasan da ake kira mafi tsada a kwallon kafa, domin wanda ya yi nasara a karawar cike gurbin, zai samu aƙalla fam miliyan 110 a kuɗin watsa shirye-shiryen Premier League.

    Za a ci gaba da wasan karshe a ranar Asabar a Wembley, kuma za a sanar da lokacin fara karawar nan gaba.

    Southampton ta amince da karya dokokin EFL dangane da yin bidiyo ba tare da izini ba na atisayen sauran kungiyoyi,” kamar yadda EFL ta bayyana, sannan an kuma gargaɗi ƙungiyar da guji aikata laifi irin wannan a bana.

    Majiyoyi sun tabbatar wa BBC Sport cewa Southampton za ta ɗaukaka kara ranar Laraba, tana mai cewa hukuncin ya wuce kima.

  10. Manchester City za ta maye gurbin Guardiola da Maresca, Manchester City

    Enzo Maresca na dab da maye gurbin Pep Guardiola a matsayin kocin Manchester City, kafin fara kakar wasa mai zuwa.

    Kamar yadda BBC Sport ta ruwaito a ranar Litinin, ana sa ran Guardiola zai bar ƙungiyar bayan wasan da za su buga da Aston Villa ranar Lahadi a filin wasa na Etihad, wanda zai zama na karshe da zai ja ragamar City.

    Maresca, tsohon kocin Chelsea shi ne aka fi ganin zai gaji fitaccen kocin ɗan kasar Sifaniya domin kakar 2026–27.

    Tun fiye da wata shida, City take ta shirye-shiryen yadda za ta yi ban kwana da Guardiola a karshen kakar nan, kuma tattaunawa da Maresca ta yi nisa.

    Kocin mai shekaru 46 yana son aikin, kuma ana sa ran nan gaba kaɗan za a tabbatar da shi a matsayin magajin Guardiola.

    Maresca ya taɓa aiki a City a baya. Ya kasance mataimakin Guardiola a kakar 2022–23 lokacin da ƙungiyar ta lashe kofuna uku, sannan ya taka muhimmiyar rawa a makarantar horas da matasan ƙungiyar kafin ya shiga babbar ƙungiyar City.

    Tsohon ɗan wasan wanda ya taɓa taka leda a West Bromwich Albion da Juventus ya bar City a 2023 domin horas da Leicester City, inda ya jagoranci kungiyar zuwa samun tikitin Premier League a kakarsa guda ɗaya.

    A kakarsa daya tilo a Stamford Bridge tare da Chelsea, ya lashe FIFA Club World Cup da UEFA Europa Conference League tare da samun gurbin shiga Champions League.

  11. , Daga Jaridu

    Ɗan wasan bayan Netherlands Lutsharel Geertruida da ke taka leda a matsayin ɗan wasan Aro a Sunderland daga RB Liepzig, na son ganin ya ci gaba da taka leda a gasar Firimiya a kakar wasa mai zuwa, dai-dai lokacin da Everton ke son ɗaukar sa. (Football Insider)

    Real Madrid da Antonio Rudireger za su sanya hannu kan tsawaita kwantaragin ɗan wasan da shekara guda, sai dai Madird na nan kan bakanta na ɗauko mai tsaron bayan Manchester City Josko Gvardiol. (AS - in Spanish)

    Mai tsaron ragar Ingila Tom Heaton, na shirin tsawaita kwantaraginsa na ci gaba da zama a Manchester United a tsawon kakar wasanni shida. (Mirror)

    Liverpool na harin ɗauko ɗan wasan Inter Milan da Nethrlands Denzel Dumfries don ɗinkin bayan ƙungiyar ta gefe. (Football Insider)

  12. Ronaldo zai buga wa Portugal gasar kofin duniya karo na shida, Gasar kofin duniya

    Cristiano Ronaldo zai buga gasar FIFA World Cup 2026 karo na shida a tarihi, bayan da aka saka shi cikin tawagar Portugal, domin wakiltarta a wasannin da za a yi a Amurka da Canada da kuma Mexico.

    Mai shekara 41 yana rike da tarihin mafi yawan buga wa kasa wasa sau 226, kuma mafi yawan ci mata ƙwallaye 143. Yana cikin ƴan wasa shida da suka taɓa buga gasar kofin duniya sau biyar a tarihi.

    A cikin wannan rukuni akwai tsohon abokin hamayyarsa a La Liga, Lionel Messi, wanda shi ma ake sa ran zai buga kofin duniya karo na shida.

    Ronaldo, wanda ya lashe ƙyautar Ballon d'Or sau biyar, yana taka leda a ƙungiyar Al-Nassr ta ƙasar Saudiyya tun daga Janairun 2023.

    Tawagar ta kuma haɗa da Bruno Fernandes, wanda ke neman kafa tarihin mafi yawan bayar da ƙwallaye a zura a raga a kakar nan Premier League, yayin da Manchester United za ta buga wasanta na ƙarshe a kakar bana a ranar Lahadi.

    A gefe guda kuma, ƴan wasan Paris Saint-Germain guda huɗu — Vitinha, Joao Neves, Nuno Mendes da Goncalo Ramos — za su buga wasan ƙarshe a Champions League da Arsenal ranar 30 ga watan Mayu, za su je wasannin gasar bana ta kofin duniya.

    Portugal za ta buga wasan sada zumunci da Chile da Najeriya kafin buɗe wasan farko a cikin rukuni da Jamhuriyar Congo a Houston ranar 17 ga watan Yuni.

    Sannan za ta kara da Uzbekistan a Houston kafin ta kammala wasannin cikin rukunii da Colombia a Miami.

    Ƴan wasan Portugal da za su buga mata kofin duniya:

    Masu tsaron raga: Diogo Costa (Porto), Jose Sa (Wolves), Rui Silva (Sporting), Ricardo Velho (Genclerbirligi).

    Masu tsaron baya: Diogo Dalot (Manchester United), Matheus Nunes (Manchester City), Ruben Dias (Manchester City), Nelson Semedo (Fenerbahce), Joao Cancelo (Barcelona), Nuno Mendes (Paris St-Germain), Goncalo Inacio (Sporting), Renato Veiga (Villarreal), Tomas Araujo (Benfica).

    Masu buga tsakiya: Ruben Neves (Al-Hilal), Samu Costa (Mallorca), Joao Neves (Paris St-Germain), Vitinha (Paris St-Germain), Bruno Fernandes (Manchester United), Bernardo Silva (Manchester City).

    Masu cin ƙwallye: Cristiano Ronaldo (Al-Nassr), Joao Felix (Al-Nassr), Francisco Trincao (Sporting), Francisco Conceicao (Juventus), Pedro Neto (Chelsea), Rafael Leao (AC Milan), Goncalo Guedes (Real Sociedad), Goncalo Ramos (Paris St-Germain).

  13. Wasannin da za a buga ranar Talata, Premier League

  14. Arsenal yanzu ta san cewa idan ta yi nasara a ranar Lahadi a kan Crystal Palace za ta lashe Premier League na Ingila na bana.

  15. An tashi wasan Arsenal 1-0 Burnley, Arsenal 1-0 Burnley

    Arsenal na daf da lashe Premier League, watakila a ranar karshe a karon farko tun bayan 2004.

  16. Mikel Arteta, Arsenal 1-0 Burnley

    Mikel Arteta ya yi canji biyu

    Leandro Trossard da Martin Odegaard sun fita an maye gurbinsu da Gabriel Martinelli da kuma Martin Zubimendi.

  17. Katin gargadi, Arsenal 1-0 Burnley

    Dan wasan Burnley, Zian Flemming ya yi karo ya samu kwallo sai ya yi karo da David Raya lokacin da suka tsalle, amma golan Arsenal ya fado kasa da karfi.

    Alƙalin wasa zai iya ɗaukar mataki kan wannan karo mai ƙarfi, domin ya yi kama da keta.

  18. An yi karin lokaci na minti bakwai, Arsenal 1-0 Burnley

    Lokaci na kurewa Arsenal na bukatar cin kwallo kada a samu matsala a farke.

  19. , Arsenal 1-0 Burnley

    Dan wasan Burnley, Josh Laurent ya yi kuskure mai sauƙi inda ya ture Myles Lewis-Skelly daga baya.

    Wannan ya bai wa Arsenal damar samun bugun tazara, inda za su iya ɗaukar lokaci su tsara kai hari cikin nutsuwa.