Hotunan yadda Tsaunin Nyiragongo ya rufta a DRC
Dubban mutane ne suka tsere daga muhallansu a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo bayan da wani tsauni ya yi aman wuta kusa da birnin Goma.
Aman wutar da dutsen ya yi ya hankada giza-gizan birnin da ke gabashi, wanda ke da yawan mutane miliyan biyu.

Asalin hoton, EPA

Mutane sun yi ƙoƙarin kashe wutar a lokacin da ruwan ya kwarara ya mamaye wasu ɓangarorin birnin da tituna.

Asalin hoton, Enoch David/Reuters
Ana iya ganin wuta a tsakankanin gine-gine a birnin.

Asalin hoton, Enoch David/Reuters
Mazauna birnin sun tsere da katifunsu da sauran kayansu.

Asalin hoton, EPA

Asalin hoton, Getty Images
Bayan isa unguwannin da ke wajen birnin da filin jirgin sama da ke gabashi, a yanzu ruwan wutar ya daina kwarara.

Asalin hoton, AFP
Dubban ƴan Congo, ciki har da yara da tsoffi sun nemi mafaka a maƙwabciyarta Rwanda a lokacin da dutsen ya yi amai.
A nan suna bacci da kayayyaki a bisa wani titi a garin Gisenyi a iyakar Jamhuriyar Demokuraɗiyyar Congo.

Asalin hoton, AFP
Tsaunin Nyiragongo na ɗaya daga cikin tsaunuka da ke aman wuta a duniya - inda a nan a ke iya ganinsa dada Tsibirin Tchegera a kan Tafkin Kivu a wajen Goma.

Asalin hoton, AFP
Duka hotunan na da haƙƙin mallaka.











