KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 24/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 24 ga watan Yunin 2026.

Skip Bidiyo and continue reading
  • Ummulkhairi Aliyu
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Arsenal
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Kutama
  • xxx
  • Sadis Buba

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Gwamnatin Oyo ta saka dokar hana fita a ƙananan hukumomi 10

    ....

    Asalin hoton, Seyi Makinde/X

    Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya amince da sanya dokar hana fita na sa'o'i 16 a wasu ƙananan hukumomi 10 kan matsalar tsaro a jihar.

    Sanarwar da sakataren gwamnatin Jihar, Farfesa Musibau Babatunde ya fitar ta ce dokar za ta fara aiki daga yau, ranar Laraba, 24 ga watan Yuni, 2026, kuma za ta kasance tsakanin karfe 4 na yamma zuwa karfe 8 na safe na tsawon sa’o’i 16 a matakin farko.

    Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun hada da Oriire da Orelope da Irepo da Saki West da Saki East da Atisbo da Itesiwaju da Iseyin da Olorunsogo da kuma Atiba, musamman waɗanda ke kusa da gandun dajin Old Oyo National Park.

    Wannan mataki ya biyo bayan zanga-zangar da ta ɓarke a jihar sakamakon sace yara da malamai a yankin Oriire a watan Mayu, inda masu zanga-zangar suka buƙaci gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa domin ceto waɗanda aka sace tare da kawo karshen matsalar tsaro a faɗin kasar.

  2. 'Amurka da Isra’ila na shirin bai wa sojojin Lebanon iko a kudancin ƙasar'

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun ce Amurka da Isra’ila na nazarin wani shiri da zai bai wa sojojin Lebanon iko da wasu yankunan kudancin ƙasar, wanda a halin yanzu sojojin Isra’ila ke riƙe da su.

    Kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito cewa, bisa wannan tsari, sojojin Lebanon za su karɓi iko da yankunan ne bayan sun samu horo da kuma binciken tsaro daga Amurka domin tabbatar da cewa ba su da alaka da kungiyar Hezbollah.

    Majiyoyi sun kuma bayyana cewa Isra’ila za ta ci gaba da zama a yankunan har sai an tabbatar da cikakken tsaro kafin a miƙa su ga sojojin Lebanon.

    Sai dai kawo yanzu Amurka da Isra’ila ba su fito fili sun tabbatar da wannan shiri ba.

    A halin da ake ciki, tattaunawa tsakanin Isra’ila da Lebanon na ci gaba a birnin Washington.

    Batun janyewar sojoji da kuma dakatar da rikici a dukkan ɓangarori, ciki har da Lebanon, na daga cikin muhimman batutuwan da ke cikin yarjejeniyar fahimta tsakanin Amurka da Iran.

  3. Kawo ƙarshen yaƙi a Lebanon tamkar kawo ƙarshen yaƙi a ƙasarmu ne - Iran

    ....

    Asalin hoton, IRNA

    Shugaban Majalisar Dokokin Iran, Mohammad Baqer Qalibaf, ya ce kawo ƙarshen yaƙi a Lebanon abu ne mai muhimmanci ga gwamnatin Tehran wanda yake tamkar kawo ƙarshen yaƙi a Iran ne.

    Ya bayyana wannan matsayi ne yayin wani jawabi a taron ƙungiyar majalisun dokoki na ƙasashen Kungiyar Hadin Kan Musulunci (OIC) da aka gudanar a birnin Baku.

    A cewarsa, Iran a shirye take ta inganta hulɗa da sauran ƙasashen Musulmi bisa ginshiƙin girmama juna da kauce wa tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kowace ƙasa.

    Haka kuma Qalibaf ya jaddada cewa tsaron yankin ya kamata ya fito daga cikin ƙasashen yankin kansu, ba tare da dogaro da karfin waje ba, yana mai nuni da cewa su ne suka fi dacewa wajen samar da tabbataccen tsaro.

  4. Trump ya soki matakin majalisar dattawan Amurka kan hana yaƙi da Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi kakkausar suka kan matakin da Majalisar Dattawan Amurka ta ɗauka na zartar da ƙudirin dakatar da matakin soja kan Iran.

    Trump ya bayyana cewa sanatoci sun aika saƙo ga Iran cewa ba su gamsu da matakan da ya ɗauka kansu ba, yana mai cewa hakan ya “tallafa tare da karfafa gwiwar abokan gaba.”

    Majalisar Dattawan Amurka ta amince da ƙudirin da ke buƙatar Trump ya dakatar da duk wani yaƙi da Iran ko kuma ya nemi izinin Majalisar Dokoki kafin ya ci gaba da ɗaukar irin wannan mataki.

    Tun da farko ma, Majalisar Wakilai ta Amurka ta amince da irin wannan kudiri.

    Sai dai ƙudirin ba ya da cikakken karfin doka, domin ana kallonsa a matsayin na alama ne kawai.

  5. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiya

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.