Kwana uku a jere ba a samu sabbin masu cutar korona a Abuja ba

Asalin hoton, Getty Images
Kwana uku kenan a jere ba a samu sabbin masu dauke da cutar korona a Babban Birnin Tarayyar Najeriya ba.
Alkaluma na karshe da hukumar yaki da cututtuka a Najeriya, NCDC, ta fitar ranar Litinin sun nuna cewa an samu sabbin mutum 20 da suka kamu da cutar a jihohin Lagos da Edo da Kano da Ogun da kuma Ondo.
Gabanin sanarwar ta ranar Litinin, NCDC, ta fitar da sanarwa sau biyu wadanda suka nuna babu sabbin masu dauke da cutar ta korona a Abuja.
Sai dai duk da haka, Abuja ce ta biyu a Najeriya cikin jihohin da ke fama da cutar korona inda take da mutum 56, yayin da jihar Lagos, wacce ita ce ta daya, take da mutum 189 da suka kamu da cutar ya zuwa ranar Litinin da maraice.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
- Lagos- 189
- FCT- 56
- Osun- 20
- Edo- 14
- Oyo- 11
- Ogun- 9
- Bauchi- 6
- Kaduna- 6
- Akwa Ibom- 5
- Katsina-5
- Kwara- 4
- Ondo- 3
- Delta- 3
- Kano- 3
- Enugu- 2
- Ekiti- 2
- Rivers-2
- Benue- 1
- Niger- 1
- Anambra- 1


Karin labaran da za ku so ku karanta








