Kwana uku a jere ba a samu sabbin masu cutar korona a Abuja ba

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Kwana uku kenan a jere ba a samu sabbin masu dauke da cutar korona a Babban Birnin Tarayyar Najeriya ba.

Alkaluma na karshe da hukumar yaki da cututtuka a Najeriya, NCDC, ta fitar ranar Litinin sun nuna cewa an samu sabbin mutum 20 da suka kamu da cutar a jihohin Lagos da Edo da Kano da Ogun da kuma Ondo.

Gabanin sanarwar ta ranar Litinin, NCDC, ta fitar da sanarwa sau biyu wadanda suka nuna babu sabbin masu dauke da cutar ta korona a Abuja.

Sai dai duk da haka, Abuja ce ta biyu a Najeriya cikin jihohin da ke fama da cutar korona inda take da mutum 56, yayin da jihar Lagos, wacce ita ce ta daya, take da mutum 189 da suka kamu da cutar ya zuwa ranar Litinin da maraice.

  • Lagos- 189
  • FCT- 56
  • Osun- 20
  • Edo- 14
  • Oyo- 11
  • Ogun- 9
  • Bauchi- 6
  • Kaduna- 6
  • Akwa Ibom- 5
  • Katsina-5
  • Kwara- 4
  • Ondo- 3
  • Delta- 3
  • Kano- 3
  • Enugu- 2
  • Ekiti- 2
  • Rivers-2
  • Benue- 1
  • Niger- 1
  • Anambra- 1

Karin labaran da za ku so ku karanta