Fati Washa ta lashe kyautar gwarzuwar jaruman Hausa a Birtaniya

Fati Washa

Asalin hoton, @washafati

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 2

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa Fatima Abdullahi da ake kira Fati Washa ta lashe kyautar gwarzuwar jaruman Hausa a wani kasaitaccen bikin fina-finan Afirka da aka gudanar a Birtaniya.

An sanar da Washa ne a matsayin gwarzuwar jaruma a taron karrama 'yan Fim da aka gudanar ranar Asabar a birnin London.

Bikin wanda ake kira Afro Hollywood Awards ya shafi karrama jaruman fina-finan harsunan Najeriya guda uku Hausa da Yoruba da Igbo da kuma na Inglishi a sassan kasashen Afirka,

Fati Washa ta lashe kyautar ne saboda rawar da ta taka a Fim din 'Sadauki.'

Jarumar ta doke Aisha Aliyu Tsamiya a Fim din da ta fito "Jamila" da kuma Halima Yusuf Atete da ta fito a "Uwar Gulma"

Rahama Sadau ta wallafa hoton bidiyo a shafinta na Instagram, lokacin da Washa ta ke karbar kyautar, inda ta bayyana farin cikinta da godiya.

Kauce wa Instagram, 1
Ya kamata a bar bayanan Instagram?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da Instagram suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Instagram da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a Instagram, 1

Ita ma Washa ta sake wallafa bidiyon a shafinta na Istagram.

Kauce wa Instagram, 2
Ya kamata a bar bayanan Instagram?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da Instagram suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Instagram da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a Instagram, 2

Washa ta ce ta sadaukar da wannan kyautar ga masoyanta tare da gode ma su, kamar yadda ta wallafa a shafinta na Facebook da ba a tantance ba.

Kauce wa Facebook

Babu karin bayanai

Ci gaba da duba FacebookBBC ba za ta dauki alhakin abubuwan da wasu shafukan daban suka wallafa ba.

Karshen labarin da aka sa a Facebook

Karo na 23 ke nan da ake gudanar da bikin karrama 'yan fim din wanda jaridar African Voice Newspapers a Birtaniya da gidauniyar Esther Ajayi da Ned Nwoko ke daukar nauyi.

Wadanda ke shiryawa da daukar nauyin bayar da kyautar a Birtaniya sun ce Sama da fina-finai 500 ne daga Afirka suka shiga gasar wacce aka fara a 1996.