Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
An cimma matsaya a rikicin Sudan
Majalisar sojoji mai mulki a Sudan da shugabannin adawa sun sa hannu a kan wata yarjejeniyar raba iko bayan kashe dare suna tattaunawa.
An sa hannu kan yarjejeniyar ne a Khartoum, babban birnin kasar a gaban masu shiga tsakani na Kungiyar Kasashen Afirka.
Kamfanin dillancin labarai na AFP sun ruwaito Mohamed Mohamed Hamdan "Hemeti" Dagolo na cewa wannan wani al'amari ne na tarihi a kasar.
Ya ce "ina farin ciki yi wa 'yan Sudan albishir kan wannan babban al'amari na sa hannu kan yarjejeniyar siyasa."
Sojoji dai sun kwace mulkin ne bayan sauke Omar al-Bashir a watan Afrilu.
Ana sa rai wannan yarjejeniya za ta kawo karshen tashin hankalin da kasar ta fuskanta a baya-bayan nan, kuma za a kafa gwamnati hadin gwiwa ta shekara uku inda kuma daga karshe za a gudanar da zabe.
Sai dai wata mai magana da yawun daya daga cikin manyan kungiyoyin fararen hula ta nuna halin ko in kula kan yarjejeniyar.
"Ba wani abin a zo a gani bane," in ji Dakta Sara Abdelgalil, kakakin kungiyar kwadago ta Sudan Professionals Association.
"Wannan shi ne matakin farko na raba iko, amma babu bayanai sosai a kansa. Mataki na biyu na tattaunawa shi ne ayyanawa a hukumance. Wannan matakin ne na fargaba da fata. Babu wani abin murna a cikinsa."