Gwamnatin Najeriya ta ce an yanke wa mutum 150 hukunci daga cikin 600 da ake zargi da ayyukan ta'addanci a ƙasar.
Babban lauyan gwamnatin ƙasar Lateef Fagbemi ya shaida wa ƴan jarida cewa an saurari shari'o'i na mutum kusan 300 cikin kwanaki biyu.
Ministan Shari'a Lateef Fagbemi, ya ce an fara zaman shari'un ne daga ranar Litinin zuwa Talata, inda ake sa ran ƙarin wasu mutum 84 da ake zargi za su gurfana a gaban kotu a ranar Laraba.
Ɗaya daga cikin waɗanda aka yankewa hukunci shi ne Ali Mustapha, wani manomi mai shekaru 55 daga Jihar Borno, wanda kotun ta yanke wa hukuncin ɗaurin shekaru 15 ba tare da zaɓin tara ba, bayan ta same shi da laifin ɓoye bayanai kan ayyukan ƙungiyar Boko Haram a ƙauyensu na Katara.
Haka kuma kotun ta yanke wa Isa Isiaka, hukuncin ɗaurin shekaru 20 a gidan yari saboda kin sanar da gwamnati bayanan da ya sani game da ayyukan ƙungiyar Boko Haram.
Ana gudanar da shari'un ne ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro, tare da sa ido daga masu lura da shari'a na cikin gida da na ƙasashen waje, ciki har da ƙungiyar lauyoyi ta ƙasar NBA da hukumar kare haƙƙin ɗan adam.
A cewar gwamnati, daga cikin shari'u 508 da suka shafi ta'addanci da aka gabatar a watan Afrilu, an samu hukunci kan mutum 386, inda aka yanke musu hukuncin ɗauri daga shekaru biyar zuwa ɗaurin rai da rai.
An mayar da zaman shari'un daga Kainji da ke Jihar Neja zuwa Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja. Fagbemi ya ce gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar murkushe ta'addanci da duk wasu ayyukan da ke da alaƙa da shi a faɗin ƙasar.
Rahotanni sun ce tun daga shekarar 2017, an yanke hukuncin dauri kan ɗaruruwan masu laifukan da suka shafi ta'addanci. Kafin waɗannan shari'u da ake gudanarwa, hukumomin ƙasar sun ce tuni aka ɗaure sama da mutum 700 kan laifukan ta'addanci.