Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Yadda sojojin Najeriya suka kubutar da matar marigayi Janar Rabe Abubakar
Gwamnan jihar Katsina Dikko Umaru Radda, ya yi wa BBC Hausa karin bayani kan yadda jami'an tsaro suka samu nasarar kubutar da Hajiya Amina Abubakar, matar marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, bayan makwanni da aka shafe ana neman ta tun bayan da ƴan bindiga suka yi garkuwa da ita tare da mijinta a yankin Matazu na jihar.
A ranar Litinin ne Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da ceto Hajiya Amina a wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce haɗin gwiwar dakarun Operation Fasan Yamma da Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ya kai ga samun nasarar kubutar da ita bayan wani samame da aka kai kan maboyar masu garkuwa da mutanen.
Tun da fari dai, sace tsohon babban Janar din sojin da matarsa da kuma mutuwarsa a hannunsu ya ja hankalin jama'a a fadin Najeriya, musamman ganin irin gudunmawar da marigayin ya bayar a fannin aikin soja da harkokin tsaro a lokacin da yake bakin aiki.
A cewar gwamnan jihar Katsinan Dikko Umaru Radda, bayan samun bayanan sirri kan motsin ƴan bindigar da kuma shirinsu na sauya mata wuri daga inda ake tsare da ita a baya, sai ya sanar da jami'an tsaro wadanda su kuma nan da nan suka kaddamar da sumame kan 'yan fashin dajin yayin da suke dauke da ita a kan babur.
Gwamnan ya ce wannan matsin lamba da dakaru suka ci gaba da yi ne ya rage wa ƴan bindigar damar motsi, lamarin da ya tilasta musu sauya maboyarsu akai-akai domin kauce wa kama su.
Sanarwar da rundunar sojin Najeriyar ta fitar ta bayyana cewa yayin ci gaba da ayyukan ceto da bincike, dakaru sun yi arangama da ƴan bindigar a ƙauyen Tunga, inda aka yi musayar wuta tsakanin bangarorin biyu.
A cewar sojojin, yayin da ƴan bindigar ke ƙoƙarin tserewa daga farmakin dakarun, sun harbi Hajiya Amina kafin daga bisani su jefar da ita tare da tserewa cikin daji don tira da rayukansu.
Wata majiya daga jami'an tsaro ta shaida wa BBC cewa an samu Hajiya Amina cikin mawuyacin hali, amma tana raye, kuma yanzu haka ana kula da lafiyarta.
Ita ma sanarwar ta ce an dauki dukkan matakan da suka dace wajen tabbatar da lafiyarta, yayin da shugabannin rundunar sojin kasar ke ci gaba da sa ido kan yadda ake kula da ita.
"Sojojin Najeriya sun himmatu wajen tabbatar da cewa ta samu cikakkiyar kulawar lafiya da kuma tallafin da ya dace domin ta murmure gaba daya," in ji sanarwar.
Sai dai yayin da ake murnar kubutar da matarsa, har yanzu al'umma na jimamin rasuwar marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya mutu bayan sace shi da aka yi tare da matarsa.
Marigayin ya kasance daya daga cikin manyan sojojin da suka yi fice a Najeriya, inda ya taba rike mukamin Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro ta Najeriya.
A lokacin da yake aiki, ya kasance daya daga cikin manyan jami'an da suka rika bayyana matsayin rundunar tsaron kasar kan muhimman batutuwan tsaro da ayyukan yaki da masu tayar da kayar baya da sauran kungiyoyin masu aikata laifuka.
Mutuwarsa ta girgiza mutane da dama, inda suke ganin cewa hakan na kara nuna irin girman matsalar da ake fama da ita, da kuma nuna cewa babu wanda ya tsira daga barazanar.
A cikin shekarun baya-bayan nan, ana fuskantar karuwar hare-hare daga kungiyoyin masu dauke da makamai, lamarin da ya jawo asarar rayuka, da sace mutane da kuma raba dubban mutane da muhallansu.
Sai dai duk da haka, hukumomin tsaro na cewa suna ci gaba da kai hare-hare kan maboyar masu laifin tare da fadada ayyukan soji a yankunan da abin ya fi kamari.
Rundunar Sojin Najeriya ta ce nasarar kubutar da Hajiya Amina ba za ta sa a dakatar da ayyukan neman wadanda suka aikata laifin ba.
Ta ce dakaru za su ci gaba da gudanar da farmaki da ayyukan bincike domin gano inda ƴan bindigar suka tsere, tare da tabbatar da cewa sun fuskanci hukunci.
Rundunar ta kuma sake jaddada kudirinta na ci gaba da kawar da masu aikata laifuka da masu garkuwa da mutane ba kawai a jihar Katsina ba, har ma a sauran sassan Najeriya da ke fama da matsalolin tsaro.
A cewar jami'an tsaron, aikin ceto Hajiya Amina ya nuna yadda hadin gwiwa tsakanin rundunonin tsaro daban-daban da kuma amfani da bayanan sirri ke ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen yaki da masu aikata laifuka a kasar.