Najeriya za ta fafata da Algeria a wasan sada zumunta

Asalin hoton, Getty Images
Tawagar kwallon kafa ta Najeriya ta na Oran, domin buga wasan sada zumunta da Algeria ranar Talata.
Super Eagles ta sauka a Algeria tun a makon jiya, inda ta zauna a Constantine, wadda ta buga wasan sada zumunta da tawagar Algeria, wadda za ta buga CHAN a bana.
Sun kuma tashi wasan 2-2 da suka fafata ranar Juma;a, inda Alex Iwobi da kuma Cyriel Dessers suka ci wa Najeriya kwallayen.
Tawagogin biyu za su kece raini a yammacin Talata a filin wasa na Stade Olympique d’ Oran.
Algeria da Najeriya sun kai zagayen karawar karshe ta neman shiga gasar kofin duniya a bana, inda Kamaru ta cire Algeria, Ghana ta yi wa Super Eagles fancale.
Ranar Juma'a Algeria ta buga wasan sada zumunta da Guinea, inda ta yi nasara da ci 1-0.
Karo na hudu da Algeria ta yi nasara a jere, ita kuwa Najeriya karkashin Jose Peseiro na sa ran yin nasara ta uku.
Kungiyoyin biyu sun fafafata sau 21 a tsakaninsu, kowacce ta ci tara da canjaras uku.
Canjaras na baya da suka yi shi ne a 1993 - daga lokacin Super Eagles ta ci wasa shida daga tara.
Algeria ta doke Super Eagles a kofin Afirka a Masar a 2019 da kuma a wasan sada zumunta a 2020 a Austria.
Najeriya na fama da 'yan wasan da ke jinya da suka hada da Victor Osimhen da Umar Sadiq da kyaftin Ahmed Musa.
Tuni kuma Wilfred Ndidi da William Troost-Ekong suka bar sansanin 'yan wasa suka koma Ingila, don yin jinya.











