Abubuwan da shugabannin kasashen duniya ke cewa a kan rasuwar Sauraniya Elizabeth ta II

Sarauniya Elizabeth

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Barack Obama da Sarauniya Elizabeth
An wallafa

Shugabannin kasashen duniya da sauran jami’an diflomasiya na ci gaba da nuna alhinin game da mutuwar Sauraniya Elizabeth ta II, wacce ta rasu tana da shekara 96 a duniya.

Sun yaba da yadda ta saudakar da kai wajen gudanar da aikinta da jajircewarta da kuma kasancewarta mai fara’a da kyautatawa.

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya jagoranci  shugabannin da suka nuna alhini inda ya tuna da “Sarauniya a matsayin mai kirki” wacce ta kasance abokiyar Faransa”.

Tsohon shugaban kasar Amurka, Barack Obama ya ce Sauraniya ta ja hankalin kasashen duniya a kan yadda ta rika mulki kuma ta rika aiki ba dare ba rana.

 

"Sau da yawa mun rika ganin yadda take mu’amala da mutane inda take magana da su cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da raha,” a cewar Mr Obama,  wanda ya gana da  sarauniya a lokuta da dama.

Shugaban Amurka na yanzu Joe Biden  ya bayyana Sarauniyar a matsayin  sarauniyar da ta kafa “tarihi a zamanin nan.”

 

Da yake magana a kan ziyararsa a Birtaniya a shekarar 2021 a matsayin shugaban kasa, Mista Biden ya ce “ ta nuna mana hazakarta da kirkinta da kuma hikimarta.”

Sarauniya Elizabeth ta biyu ta gana da shugabannin Amurka 14 a lokacin mulkinta.

Tsallake Whatsapp
Tasharmu ta WhatsApp

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Latsa nan domin shiga

Karshen Whatsapp

Tsohon shugaban Amurka  Donald Trump  ya ce  " ba zan taba mantawa da kyakkyawar abota  da martaba da hikima da kuma ban dariyarta.

"Mace ce mai kyau- babu kamarta!,” kamar yadda ya bayyana a sakon da ya rubuta  a shafinsa na Truth Social.

Haka kuma a lokacin mulkinta ne  firaiministoci 12 na Kanada suka yi mulki.

A jawabinsa jim kadan bayan da aka ba da labarin rasuwarta, Justin Trudeau ya ce mutanen Canada suna nuna alhininsu.

“Ta kasance daya daga cikin mutanen da na fi so a duniya, kuma za mu yi kewarta”, in ji shi.

'Sauraniya ce da babu kamarta '

 

Sarki Netherlands  Willem-Alexander  -  wanda dan uwan sarauniya Elizabeth na biyar ne  - ya ce shi da sarauniya  Maxima za su tuna da ita a matsayin “Sarauniya mai hikima, mai matukar girmamawa da kauna”.

Shi ma Sarki Philippe da Sarauniya Mathilde na Belguim sun ce “shugaba ce da kasafai ake ganin irinta ba  wacce  a tsawon lokacin da ta shafe kan mulki ta nuna mutunci da jajircewa da sadaukarwa”.

Firaiministan Indiya Narenda Modi ya tuna da taron da ba zai taba mantawa da shi ba da sarauniya a ziyararsa zuwa Birtaniya

 

"Ba zan manta da karamcinta ba da kyautatawarta,” kamar yadda ya bayyana a sakon da ya wallafa a shafin Tuwita.

  

Shugaban gwamnatin Jamus  Olaf Scholz  ya jinjina wa Sauraniyar yana mai cewa “aniyar da ta nuna wajen ganin Jamus da Birtaniya sun sasanta bayan abubuwa masu tayar da hankali da suka faru a lokacin Yakin Duniya na Biyu abu ne da ba za a manta da shi ba.”

  

An samu gagarumin sauyi a mulkinta

A matsayinta na sarauniyar da ta shafe shekara 70 kan mulki Sarauniya Elizabeth ta yi rayuwa a cikin wani lokaci na sauyi kamar yadda aka bayyana a sakonin ta’aziyya.

Kamar yadda Barack Obama ya bayyana “ta yi rayuwa a lokutan wadata da rikice-rikice kama daga lokacin da bil adama ya sauka a wata da kuma faduwar katangar Berlin”.

Sakatare janarar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres ya ce a zamanin mulkinta  ne aka samu gagarumin sauyi ciki har da  bai wa kasashen Afrika da Asiya ‘yancin kai da kuma farfadowar kungiyar Commonwealth”.

“Sadaukarwar da ta yi ta tsawon rayuwarta wajen yi wa al’ummarta hidima abar sha’awa ce”

Shugaban Isra’ila Isaaz Herzog ya ce duk da cewa an samu gagarumin sauyi a lokacin mulkinta amma duk  tsawon wannan lokaci “ta kasance abar koyi mai nagarta, mai rikon amana mutuntaka da kishin kasa.”

Ko da yake Sarauniyar ba ta ziyarci Isra’ila ba, Charles, Edward, William  da marigayi  Philip – wanda aka binne mahaifiyarsa a birnin Kudus, sun je.

"Sauraniya  Elizabeth  ta  kafa tarihi kuma ko a mutuwarta ma ta bar abubuwa da za a yi koyi da su,”a cewar Shugaba Herzog.