Arsenal ta bai wa Man City tazarar maki takwas a Premier

Arsenal

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

Arsenal ta doke Crystal Palace da ci 4-1 a wasan mako na 28 a gasar Premier League da suka kara ranar Lahadi a Emirates.

Arsenal ta ci kwallayen ta hannun Gabriel Martinelli da Granit Xhaka da kuma Bukayo Saka da ya zura biyu a raga.

Kenan Saka ya ci kwallo 13 a dukkan karawa a bana a Arsenal har da 12 a Premier League - kakar da ya ci kwallo da yawa kenan.

Ita kuwa Palace ta zare daya ta hannun Jeff Schlupp, bayan da suka koma hutu a zagaye na biyu kenan.

Arsenal ta ci wasa 22 kenan a babbar gasar Premier League ta kakar nan, fiye da wadanda ta ci a bara.

Gunners ta hada maki 69 kenan ta ci gaba da zama ta daya a teburi da tazarar maki takwas tsakaninta da Manchester City ta biyu mai maki 61.

Ta ci wasa shida a jere a bana ta kuma yi bajintar Newcastle Uniteda, wadda ta yi hakan tsakanin Oktoba zuwa Disambar 2022.

Mikel Arteta

Asalin hoton, Getty Images

Haka kuma karo na biyu kenan da ta yi nasara a wasa a shida a jere a Premier League karkashin Mikel Arteta.

Palace wadda ta buga wasan karkashin kociyan matasanta 'yan shekara 21, Paddy McCarthy, bayan da ta kori Patrick Vieira tana ta 12 a teburi da maki 27.

Tazarar maki uku ne tsakaninta da West Ham ta ukun karshe mai kwantan wasa mai maki 24.

Manchester City mai kwantan wasa daya ta ci Burnley 6-0 ranar Asabar ta kai daf da karshe a FA Cup na bana.

Arsenal wadda rabon ta dauki Premier League tun 2004 karkashin Arsene Wenger, am fitar da ita daga Europa League a hannun Sporting.

Haka kuma City ce ta cire ta a FA Cup, sannan Manchester United ta lashe Carabao Cup na bana.

Saura wasa 10 a kammala kakar bana, ranar Asabar 1 ga watan Afirilu, Gunners za ta karbi bakuncin Leeds United a wasan mako na 29 a gasar Premier League.