Abun fashewa ya tashi a wani kasuwa a Lagos

Asalin hoton, Screengrab/Lagos Police Command
Abun fashewa ya tashi a wani sashe na kasuwar Mushin da ke Lagos a ranar Litinin, inda mutum guda ya jikkata bayan wata mota ta tarwatse sakamakon fashewar.
Lamarin ya faru ne da tsakar dare a wani wuri da ke 22, Oke Mushin, inda aka ajiye motar a cikin kasuwar kayan takalma.
Mazauna yankin sun bayyana cewa ana zargin wani ne ya dasa abun fashewa (IED) a ƙarƙashin motar da ta tarwatse, amma har yanzu ba a gano mamallakin motar ba.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Fatai Tijani, ya ce sun samu rahoton fashewar, kuma nan take suka tura ƙwararrun jami’an kwance abubuwan fashewa (EOD) zuwa wurin.
Ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna cewa an sanya IED ɗin ne a ƙarƙashin motar a ɓangaren fasinja, kuma ya fashe ne a lokacin da aka kunna injin motar.
















