Senegal 0-1 Aljeriya
Aljeriya ta yi laifi a wannan wasa sau tara sama da Senegal da ta yi biyar.
Yanzu haka Lamine Gassama ne a kwance bayan Ismael Bannacer ya kai shi kasa.
Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Labarai da bayanai kai-tsaye game da wasan karshe a Gasar Cin Kofin Kasashen Afirka AFCON 2019.
Umar Rayyan and Umar Mikail
Aljeriya ta yi laifi a wannan wasa sau tara sama da Senegal da ta yi biyar.
Yanzu haka Lamine Gassama ne a kwance bayan Ismael Bannacer ya kai shi kasa.
Bugun tazara ne Senegal ta samu bayan an buge Mane a kusa da yadi na 27.
Kuma an buga M'Bolhi ya kama
Zuwa yanzu Senegal ce kan gaba wajen yawan rike kwallo da kashi 53%, inda Aljeriya ke da kashi 46%
Senegal ta samu bugun tazara amma Aljeriya ta cire kwallon.
Wasa yana ci gaba da daukar zafi kowa yana kai wa kowa hari akai-akai.
Aljeriya ta samu bugun tazara amma Senegal ta cire kwallon.
Aljeriya ta jefa kwallo a ragar Senegal ta hannun Baghdad Bounedjah ana cikin minti biyu da fara wasa.
Senegal ta fara kai wa Aljeriya hari
An fara wasa tsakanin Senegal da Aljeriya.
Kokarin gololin kasashen biyu...
Duka kocin Senegal da na Aljeriya suna horar da tawagar kasashensu ne. Kuma duk kasar da ta yi nasara ta kafa tarihi ke nan.
Ita ma kungiyar Everton ta yi wa dan wasanta Idrissa Gana Gueye wanda dan Senegal ne fatan lashe wannan kofin.
Haka zalika kungiyar Manchester City Riyad Mahrez ta yi wa Mahrez fatan samun nasara a wasan a shafinta na Twitter.
Kungiyar da dan wasan Senegal Sadio Mane ke yi wa wasa a Turai, Liverpool, ta yi wa shahararren dan wasan fatan nasara a karawar yau a shafinta na Twitter.
'Yan wasan Najeriya sun koma gida a ranar Juma'a.
Najeriya ce ta zo ta uku a gasar bayan doke Tunisiya da ci 1-0 a ranar Laraba.
A karshen makon jiya ne Aljeriya ta doke Najeriya da ci 2-1 a wasan kusa da na karshe.