A saƙonsa na jimami da alhinin rasuwar Sarauniyar
Ingila Elizabeth, Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce ya ji baƙin ciki matuka
da samun labarin mutuwar Sarauniyar.
Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a wata sanarwa
da mai taimaka masa kan yaɗa
labarai Malam Garba Shehu ya fitar jiya Alhamis.
"Ni da iyalaina da al'ummar
Najeriya sama da miliyan 200 duk mun ji takaici sosai na rasuwar Sarauniya Elizabeth, wanda hakan ya kawo ƙarshen mulkinta na tsawon shekara 70 mai cike da ban
sha'awa da babu irin sa.
“Mulkin marigayiyar shi ne
kadai masarauta mai girma a Turai da kashi 90 cikin 100 na al'ummar duniya a
yau da suka sani.”
Ya ƙara da cewa “a daidai wannan lokaci na jimami
mun bi sahun sauran ƙasashen duniya wajen
alhinin rashin Sarauniya Elizabeth.
"Muna miƙa ta’aziyyarmu ga illahirin iyalan masarautar
da mutanen ƙasar Birtaniya da ma ɗaukacin ƙasashe Rainon Ingila na (Commonwealth).”
Shugaba Buhari ya ce tarihin
Najeriya a matsayin ƙasa ba zai taɓa kammaluwa ba, ba tare da an
taɓo babin Sarauniya Elizabeth ta biyu ba, shugabar da
zamto tamkar wata bango ga ƙasashen duniya ta
kuma yi fice da shahara.
“Ta sadaukar da rayuwarta wajen
gina ƙasarta da ƙasashe rainon Ingila da ma ƙoƙarin tabbatar da duniya ta zama
waje mai kyau", sanarwar ta ƙara da cewa.
Shugaba Buhari ya yi maraba da
Mai Girma Yarima Charles bisa gadon mulkin da ya yi, ya kuma yi addu'ar ganin
ci gaba da samun ƙarin ingantuwar dangantaka da
alaƙa tsakanin ƙasashen biyu a yayin mulkin
Yarima Charles na III.