Ahmed Lawan shi ne na biyu da ya soma jawabi, inda shi ma ya ce ya cancanta ya zama shugaban ƙasa
A cewarsa, ya shekara 23 a majalisa kuma a cewarsa yana da ƙwarewar da zai jagoranci Najeriya.
Ya bayyana cewa ko a ƙasashen da suka ci gaba, akwai da dama daga cikin waɗanda suka zama shugaban ƙasa da ƴan majalisa ne inda ya ce hakan ya sa ya cancanci zama shugaban ƙasa.
Ya bayyana cewa idan aka zabe shi, zai ɗora daga kan manyan ayyukan da shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya yi wa Najeriya
Ya kuma bayyana cewa irin dabarun da aka yi amfani da su wurin yaƙar ƴan Boko Haram a Arewa Maso Gabas, za su yi amfani da irin waɗannan dabaru domin yaƙar ƴan bindiga da ke Arewa Maso Yammacin Najeriya