Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Atiku ya fi karfin Tinubu, in ji PDP

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita, Umar Mikail, Umaymah Sani Abdulmumin, Halima Umar Saleh and Nasidi Adamu Yahaya

  1. Deliget daga Jihar Yobe ma sun saka takalmansu

    Deliget daga Jihar Yobe ma sun saka takalmansu don fita wajen jefa ƙuri'a.

    Mutum 51 aka tantance da za su kaɗa ƙuri'un nasu daga jihar tsohon shugaban APC na riƙo Gwamna Mai Mala Buni.

    Mista Buni ne zai sake yi wa APC takarar gwamna a Yobe a babban zaɓen mai zuwa a 2023.

  2. Deliget ɗin Taraba ma an kira su

    Jihar Taraba na da jumillar deliget 46 da aka tantance daga cikin 48.

  3. Deliget daga Ekiti sun fito

    Wakilai masu kaɗa ƙuri'a daga Jihar Ekiti a kudu maso yammacin Najeriya sun fito don yin aikinsu na jefa ƙuri'a.

    Mutanen 48 da aka tantance sun fito ne daga jihar da ɗan takara Gwamna Kayode Fayemi ya fito, kodayake ya janye wa Bola Ahmed Tinubu tun kafin fara kaɗa ƙuri'ar.

  4. Wace irin ƙuri'a ake jefawa?

    Zaɓen fitar da gwanin da APC ke gudanarwa ba irin sauran zaɓuka ba ne idan ana maganar takardar jefa ƙuri'a.

    A wannan zaɓen, akan ba wa daliget farar takarda ne, inda shi kuma zai rubuta sunan ɗan takarar da yake so a jiki kuma ya jefa a akwati.

    Sai dai kuma daliget ɗin da ba su iya rubutu ba, suna da damar neman taimako daga wajen ɗan uwansu daliget na jihar da suka fito don ya taya su rubutawa.

    Kazalika, an gargaɗe su cewa su rubuta cikakken sunan ɗan takara saboda akwai sunaye kamar "Ahmed" da 'yan takara uku ke da shi, da kuma "farfesa" biyu.

  5. An umarci wakilan Sokoto su fito

    Jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya na da jumillar daliget 69 da za su kaɗa ƙuri'a.

  6. Deliget daga Edo na fitowa

    Jihar Edo na da adadin masu jefa ƙuri'a 52 da aka tantance daga 57.

  7. An nemi deliget daga Jihar Enugu su fito

    Yanzu kuma wakilan Jihar Enugu ne daga kudu maso gabashin Najeriya za su fito don jefa nasu ƙuri'un.

    Deliget ɗin 51 ne za su zaɓa su darje.

  8. Jiha 12 sun kaɗa ƙuri'unsu zuwa yanzu

    Wakilai daga jihohi 12 ne suka kaɗa ƙuri'unsu zuwa yanzu yayin da jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ke ƙoƙarin zaɓar ɗan takararta na shugaan ƙasa a zaɓen 2023 mai zuwa.

    Jihohin su ne Abiya da Kano da Adamawa da Katsina da Delta da Cross River da Osun da Ogun da Borno da Neja.

    Sauran su ne Binuwai da Nasarawa da Bauchi.

    Yawan daliget da suka jefa ƙuri'a zuwa yanzu

    • Abiya 50
    • Adamawa 62
    • Cross River 54
    • Delta 73
    • Ogun 60
    • Osun 90
    • Neja 75
    • Binuwai 64
    • Bauchi 55
    • Borno 81
    • Katsina 102
    • Nasarawa 39
  9. An kirawo wakilan Jihar Delta

    Daliget daga Jihar Delta a kudu maso kudancin Najeriya na gab da kaɗa ƙuri'unsu a zaɓen fitar da gwani na jam'iyyar APC mai mulki.

    Deliget 73 ne cikin 75 za su kaɗa ƙuri'u a wannan assalatun.

  10. Deliget daga Cross River ma sun fito

    Masu kaɗa ƙuri'a daga Jihar Cross River da ke kudu maso kudu na jefa ƙuri'unsu.

    Wakilai 54 ne za su yi zaɓen daga Cross River, jihar da Gwamna Ben Ayade ya fito - ɗaya daga cikin 'yan takarar.

  11. An umarci daliget ɗin Osun su saka takalmansu su fito kaɗa ƙuri'a

    Wakilai 90 daga Jihar Osun aka kirawo don kaɗa ƙuri'unsu.

  12. Wakilai daga Ogun na kaɗa ƙuri'a

    Su ma deliget daga Jihar Ogun ta kudu maso yammacin Najeriya sun himmatu wajen zaɓar nasu 'yan takarar.

    Ogun na da daliget 60 kuma dukkansu ba su yi ƙasa a gwiwa ba a daren nan wajen yin zaɓen.

  13. Daliget daga Borno sun gabato akwatin zaɓe

    Wakilai daga Jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya na kaɗa tasu ƙuri'unsu.

    Borno na da deliget 81 da aka tantance daga cikin 81 da za su yi zaɓe.

  14. Daliget daga Jihar Neja sun fito

    Su ma daliget na Jihar Neja sun saka takalmansu don zuwa kan akwatin kaɗ ƙuri'a.

    Akwai mutum 75 da aka tantance don kaɗa ƙuri'a daga Jihar Neja.

  15. Daliget daga Jihar Binuwai na jefa ƙuri'a

    Masu zaɓe daga Jihar Binuwai a yankin arewa ta tsakiyar Najeriya na jefa ƙuri'unsu a zaɓen fid da gwani na jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar.

    Binuwai na da daliget 64 da aka tantance daga cikin 66 da za su kaɗa ƙuri'a.

    'Yan takara 14 ne ke fafatawa a zaɓen don samun wanda zai yi wa APC takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

  16. An kirawo daliget daga Jihar Nasarawa

    Masu jefa ƙuri'a daga Jihar Nasarawa za su iya fita fili domin kaɗa nasu ƙuri'un, a cewar shugaban kwamatin zaɓe Gwamna Atiku Bagudu.

    Jihar Nasarawa na da daliget 39 kuma dukkansu aka tantance don yin zaɓen a daren nan.

  17. Za a ci gaba da jefa ƙuri'a

    Shugaban kwamatin zaɓe na taron jam'iyyar APC, Atiku Bagudu, ya ce yanzu za a ci gaba da jefa ƙuri'a bayan shawo kan wasu matsaloli.

    Ya ce jiha ta gaba da za a kira ita ce Bauchi.

    Yanzu daliget ɗin Kano ne ke kammala jefa tasu.

  18. Daliget na jiha biyar na fuskantar matsaloli

    Shugaban kwamatin zaɓen fid da gwani na jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya, Gwamnan Kebbi Atiku Bagudu, ya bayyana cewa wasu wakilai na jihohi sun yi ƙorafin samun matsala.

    Wannan na cikin dalilan da suka sa kaɗa ƙuri'a ya tsaya cak yanzu haka bayan wakilan Abiya da na Kano da Adamawa sun kaɗa ƙuri'unsu.

    Sai dai gwamnan ya ce matsalar ta faru ne tun a wajen tantancewa sannan ya nemi jihohin da ba su fuskanci matsalar ba da su ci gaba da jefa ƙuri'iunsu.

    Amma da alama matsalar ta wuce yadda aka bayyana tun farko domin kuwa yanzu haka an tsaya cak da jefa ƙur'ia.

    Wakilin BBC da ke wajen, Buhari Muhammad Fagge, ya ce da alama za a iya kaiwa ƙarfe 9:00 na hantsin Laraba ba a kammala wannan zaɓe ba.

  19. An dakatar da kaɗa ƙuri'a saboda...

    Tun daga sanda aka fara kaɗa ƙuri'a, har yanzu wakilan jiha huɗu kawai aka kirawo.

    Yanzu haka kaɗa ƙuri'ar ba ya tafiya saboda a cewar masu shirya taron mutane sun cushe wurin jefa ƙuri'ar.

    Jihohin su ne Abiya da Adamawa da Kano da Katsina.

    Akwai jiha 33 ke nan - har da birnin Abuja - nan gaba da za su fito don jefa ƙuri'unsu.

  20. Buhari da wasu 'yan takara sun fice daga wurin zaɓe

    Jim kaɗan bayan fara kaɗa ƙuri'a a wurin zaɓen fid da gwani na jam'iyyar APC mai mulki, Shugaba Muhammadu Buhari ya fice daga filin taron.

    Shugaban ya fita tare da Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan - ɗan takara - da Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo - ɗan takara - da kuma Shugaban APC na Ƙasa Abdullahi Adamu.

    Sai dai Buhari bai fice ba sai da ya yi jawabi, yana mai roƙon 'yan ƙasar da "kada ku bari (jam'iyyar adawa) PDP ta mayar da Najeriya baya".

    A gefe guda kuma, tuni jefa ƙuri'a ya yi nisa, inda daliget ke kaɗa wa 'yan takara 14 ƙuri'a.