Abubuwan da suka faru a Najeriya da Nijar da sassan duniya

Wannan shafin yana kawo muku labarai da rahotannin abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya and Nabeela Mukhtar Uba

  1. An dakatar da malaman jami’a kan zargin lalata da dalibai

    Jami’ar Ghana ta dakatar da malaman nan biyu da BBC ta bankado suna cin zarafin dalibai mata da kuma son yin lalata da su.

    Tun a watan Oktoba ne aka soma dakatar da malaman jami’ar biyu, Farfesa Ransford Gyampo da Dr Paul Kwame Butakor domin gudanar da bincike a kansu.

    Yanzu an dakatar da su na tsawon lokuta daban-daban ba tare da biyan su albashi ba.

    Wata sanarwa da jam’iar ta fitar ranar Litinin ta ce an dakatar da Farfesa Gaympo tsawon wata shida ba tare da albashi da, yayin da aka dakatar da Dr Butakor tsawon wata hudu ba tare da albashi ba.

    Dukkan su sun musanta zarge-zargen da aka yi musu.

    Kazalika, dole ne malaman su samu horo kan kaucewa cin zarafin mutane ta hanyar lalata da kuma yadda ya kamata su rika tafiyar da harkokin dalibai.

    Farfesa Gyampo da Dr Butakor ba za su koma bakin aiki ba sai an gamsu cewa sun gyara dabi’unsu.

    Farfesa Ransford Gyampo da Dr Paul Kwame Butakor
    Bayanan hoto, Farfesa Ransford Gyampo da Dr Paul Kwame Butakor sun musanta zargin
  2. Barkan mu da sake saduwa

    Sashen Hausa na BBC ne yake muku barka da wannan rana ta Talata. Da fatan za ku bibiye mu domin sanin dalin da duniya ke ciki, musamman al'amuran da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da wasu sassan duniya.

  3. Rufewa

    A nan muka kawo karshen labarai da rahotanni kai tsaye a wannan shafin.

    Sai kuma gobe Talata idan Allah ya kaimu inda za mu ci gaba da kawo wasu sabbin labaran.

    Za ku iya duba kasa domin karanta abubuwan da suka faru ranar Litinin.

  4. An kashe mutum 24 a harin Cocin Burkina Faso

    Rahotanni daga Burkina Faso sun ce akalla mutum 24 ne suka mutu a harin da aka kai a wani coci da ke kusa da kan iyakar kasar da Jamhuriyar Nijar ranar Lahadi.

    Wannan ne hari na baya-bayan nan da mutanen da ake zargi masu kaifin kishin Musulunci ne suka kai a kasar.

    Tun 2015, daruruwan mutane maharan suka kashe a Burkina Faso, sannan fiye da mutum 500,000 aka raba da muhallansu.

  5. Rundunar sojin sama ta kai wa ISWAP samame a Borno

    Rundunar sojin sama a Najeriya ta ce ta lalata sansanin horarwa na kungiyar IS da ke yankin Afirka ta Yamma wato ISWAP a Kirta Wulgo kusa da tafkin Chadi a arewacin jihar Borno.

    Air Commodore Ibikunle Daramola, shugaban sashen yada labarai na rundunar ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka fitar yau Litinin a Abuja, babban birnin Najeriya.

    Daramola ya ce an kai samamen ranar Lahadi karkashin shirin Operation Lafiya Dole.

    Ya yi bayanin cewa nasarar ta biyo bayan bayanan sirri da suka samu.

    Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa akwai wasu gine-gine da masu tada kayar bayan ke amfani da su wajen horar da mayakan.

  6. Fadar shugaban Najeriya ta ce Buhari ba zai yi tafiya ba

    Fadar shugaban Najeriya ta karyata rahotannin da ake yadawa cewa Shugaba Muhammadu Buhari zai yi wasu tafiye-tafiye.

    Mai bai wa shugaban shawara kan kafafen yada labarai Femi Adesina, ne ya musanta labaran wanda ke cewa Buhari zai fara tafiya Birtaniya inda zai shafe kwana 20 sannan daga bisani ya je Saudiyya daga nan kuma ya je birnin Austria.

    Femi Adesina wanda ya wallafa hakan a shafinsa na Facebook, ya bukaci 'yan kasar da su yi taka-tsan-tsan kan labaran da ake yadawa musamman a kafafen sada zumunta.

    Ya ce labaran kanzon kuregen da ake yadawa ba wai iyalan shugaban kasar kadai ya shafa ba, har da ministoci da manyan jami'an gwamnati da sojoji da sauran kusoshin gwamnati.

  7. Ana bincike kan badakalar makamai a Kenya

    Masu bincike a Kenya na tuhumar wani ma'aikaci a ofishin mataimakin shugaban kasar William Ruto a wani bangare na binciken da ake kan badakalar makamai ta kusan dala miliyan 400.

    A wata kotu da ke Nairobi babban birnin kasar, wani tsohon ministan wasanni Rashid Echesa, ya musanta aikata almundahana.

    Ana zarginsa da kokarin samun kudi daga dan kasuwar Poland bayan ya yi musu alkawarin zai iya samar da makamai ga sojojin Kenya.

    'Yan sanda sun ce Mr Echese ya karbi sama da dala dubu 100.

    Mr Ruto ya kuma musanta hannu a badakalar.

    Uhuru Kenyatta

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Uhuru Kenyatta
  8. Kotu ta yi watsi da karar masu nadin sarki a Kano kan kirkirar sabbin masarautu

    Wata babbar kotu a Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya ta yi fatali da karar da masu nadin sarki a jihar suka shigar don kalubalantar samar da sabbin masarautun yanka hudu da kuma nadin sarakuna masu daraja ta daya.

    Da ya ke yanke hukunci a ranar Litinin, alkali Ahmad Badamasi ya ce abubuwa da dama sun sha gaban karar yayin da dokar da ta kirkiri sabbin masarautun ta kawo karshen hukuncin alkali Usman Na'abba ranar 21 ga watan Nuwamba wanda ya soke samar da sabbin masarautun.

    Masu nadin sarkin hudu da suka shigar da karar su ne Hakimin Dawakin Tofa Yusuf Nabahani (Madakin Kano) da Hakimin Wudil Abdullahi Sarki Ibrahim (Makaman Kano) da Hakimin Gabasawa Bello Abubakar (Sarkin Dawaki Mai Tuta da Hakimin Dambatta Mukhtar Adnan (Sarkin Ban Kano).

    Premium Times ta rawaito cewa dukkan masu nadin sarkin hudu sun rasa mukaminsu na Hakimi sannan an nada wadanda za su maye gurbinsu.

    Wadanda ake kara su ne gwamnatin Kano da gwamnan jihar da shugaban majalisar dokokin Kano da majalisar dokokin jihar da alkalin alkalai na jihar.

    Kazalika akwai sabbin sarakunan Aminu Ado Bayero Sarkin Bichi da Ibrahim Abubakar Sarkin Karaye da Tafida Abubakar Sarkin Rano da Ibrahim Abdulkadir Sarkin Gaya.

    Kano

    Asalin hoton, Getty Images

  9. Coronavirus ta hana jam'iyyar kwaminisanci taronta na shekara-shekara

    Kafofin yada labarai a China sun ce za a jinkirta babban taron Jam'iyyar NPC mai bin tsarin kwaminisanci wanda ta saba gudanarwa duk shekara yayin da kasar ke fafutukar shawo kan cutar numfashi ta coronavirus.

    Za a yanke hukunci kan mataki na karshe game da jinkirta taron zuwa mako mai zuwa.

    Yanzu haka dai cutar ta kashe mutum kusan 18,000 inda sama da 70,000 suka kamu da ita.

    Fiye da mutum dubu biyu ne aka samu rahoton sun kamu da cutar a ranar Litinin.

    Kakakin Hukumar Lafiya ta Duniya, Margaret Harris, ta shaida wa BBC cewa suna marhabin da fadada hanyoyin wayar da kan jama'a game da yadda za a shawo kan cutar.

    Ta ce: "Yana da mahimmanci ace akwai tattaunawa game da dakile yaduwar cutar, kuma dukkanmu zamu iya yi, yadda zamu iya kare kanmu, misali, inganta tsabtar muhalli da tabbatar da duk abubuwan da suke kewaye da mu suna da tsabta da sauransu."

    Za a dauki matsaya kan mataki na karshe game da jinkirta taron zuwa mako mai zuwa.

    Asalin hoton, Getty Images

  10. Za a shigar da Shugaba Buhari kara kotu

    Fitaccen lauyan nan na Najeriya, Femi Falana, ya sha alwashin kai karar Shugaba Muhammadu kotu saboda ya ki sauke hafsoshin sojin kasar.

    Lauyan ya shaida wa gidan talbijin na Channels TV cewa dokokin soji sun bukaci duk sojan da ya shekara 35 yana aiki ko kuma ya kai shekara 60 a duniya, ya yi ritaya.

    Ya ce za su shigar da karar a makon gobe.

    Rahotanni sun ce hafsan tsaro, Gabriel Olonisakin; hafsan sojin kasa, Tukur Buratai; hafsan sojin sama, Sadique Abubakar da kuma hafsan sojin ruwa Ibok-Ete Ekwe Ibas sun kai shekara 35 suna aikin soji.

    Sai dai Shugaba Buhari ya sabunta wa'adin hafsoshin sojin a watan Disambar 2018 bisa la'akari da kundin tsarin mulkin soji.

    "An tsawaita wa'adin nasu ne bisa ikon da sashe na 218 (1) da (2) na kundin tsarin mulkin kasar ya bai wa shugaban kasa," a cewar sanarwar da gwamnatin Najeriyar ta fitar a wancan lokaci.

    Amma Mr Falana ya yi ikirarin cewa a cikin sashe na shida na kundin tsarin mulkin soji, wanda ya bai wa shugaban kasa damar tsara dokokin soji, babu inda aka ce zai iya kara wa'adinsu fiye da yadda aka ambata a baya.

    Falana ya ce babu dkar da ta amince Shugaba Buhari ya kara wa'adin hafsoshin soji

    Asalin hoton, Facebook/Femi Adesina

    Bayanan hoto, Falana ya ce babu dkar da ta amince Shugaba Buhari ya kara wa'adin hafsoshin soji
  11. Kotu ta haramta wa INEC soke rijistar wasu jam'iyyu a Najeriya

    Wata babbar kotu a Abuja, babban birnin Najeriya ta dakatar da hukumar zaben kasar INEC daga soke rijistar jam'iyyu 31.

    Kotun karkashin mai shari'a Anwuli Chikere ta ce hukuncin ya biyo bayan karar da jam'iyyun da aka soke rajistar tasu suka shigar gabanta.

    Mai shari'ar ta ce INEC ta gaza karyata karar da jam'iyyun suka shigar wanda ta ce dole ne a kare hakkokinsu.

    Jaridar DailyTrust ta ruwaito cewa a ranar 6 ga watan Fabrairu ne INEC ta soke rajistar jam'iyyun siyasa 74.

    Kotu

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Farfesa Mahmood Yakubu Shugaban hukumar zabe a Najeriya
  12. An bayar da lasisin rigakafin cutar Ebola a kasashen Afirka hudu

    A yanzu kasashen Afirka hudu - Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo da Burundi da Ghana da Zambia na da lasisi kuma za su iya rarraba allurar riga-kafin cutar Ebola wanda Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta bayyana a matsayin gagarumin ci gaba.

    Binciken farko da aka yi ya nuna cewa allurar Ervebo da kamfanin Merck ya yi tana da inganci sosai.

    Bayanai sun nuna cewa yi wa mutanen da suka kamu da cuta allurar rigakafi na rage yiwuwar su mutu.

    Congo a yanzu haka tana fama da barkewar Ebola da ta yi sanadiyyar halaka mutu 2,249 tun Agustan 2018.

    ''Amince da allurar riga-kafin Ebolan da kasashen suka yi wani ci gaba ne a yakin da ake da cutar,'' in ji Shugaban WHO, Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus.

    Ebola

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Allurar Ervebo na da karfin warkar da mara lafiya da kashi sama da 97
  13. An kashe mutum 22 a wani kauyen Kamaru

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce kimanin mutum 22 ne suka mutu a wani hari da aka kai wani kauye da ke arewa maso yammacin Kamaru.

    Sama da rabin mutanen da aka kashe a Ntumbo yara ne, kuma kafafen yada labaran kasar sun ce wasu da dama sun kone kurmus.

    Babu kungiyar da ta dauki nauyin kai harin na ranar Juma'a sai dai jam'iyyar hamayya na zargin rundunar sojin kasar.

    Gwamnatin Kamaru wadda ta ke yaki da 'yan aware a yankin kusan shekara uku kenan ta musanta hannu a harin.

    Kamaru

    Asalin hoton, ANADOLU AGENCY

    Bayanan hoto, An sha zargin Shugaban Kamaru Biya da take hakkokin bil adama a lokacin rikici
  14. Jam'iyyar adawa a Nijar ta mayar da martani kan rikicin cikin gida

    Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa jam'iyyar adawa ta Moden Lumana ta Hama Amadu ta mayar da martani kan wasu wasiku biyu na ministan cikin gida game da rikicin cikin gida na jam'iyyyar.

    Jam'iyyar dai ta yi kashedi kan duk wani shisshigi ko katsalandan da ta ce ministan ke kokarin yi game da rikicin shugabancin da ya dabaibaye ta.

    Moden Lumana ta yi wannan gargadi ne yayin wani taron manema labarai da ta kira.

    Ku saurari rahoton wakiliyarmu Tchima Ila Issoufou:

    Bayanan sautiLatsa alamar lasifika domin sauraron rahoton Tchima Illa Issoufou
  15. Kotu ta ba da umarnin kama Dikko Inde

    Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, babban birnin Najeriya ta bayar da sammacin kama tsohon shugaban hukumar fasa-kauri ta kasar, Abdullahi Inde Dikko.

    Jaridar The Nation, wacce ta ba da wannan labari, ta ambato kotun na yin umarnin kama shi ne saboda kin bayyana a gabanta domin fuskantar shari'a kan zarge-zargen almundahana da hukumar da ke yaki da cin hanci ta the Independent Corrupt Practices and other related offences Commission (ICPC) ke yi masa.

    Mai shari'a Ijeoma Ojukwu, wadda ta bayar da umarnin kama Alhaji Dikko ranar Litinin, ta ce a baya lauyansa Solomon Akuma (SAN) ya yi alkawarin zai kawo mutumin da yake wakilta kotun ranar Litinin, amma sai ya gabatar mata da wani rahoto daga asibit da ke nuna cewa tsohon babban jami'in na hukumar fasa-kauri ba shi da lafiya inda yake jinya a London.

    Mai shari'a Ojukwu ta ce adireshin Dikko, kamar yadda rahoton asibitin ya nuna shi ne – No: N6 Ahmed Musa Crescent Jabi, Abuja – kuma ya nuna cewa Alhaji Dikko Inde ba ya abisiti a London.

    Ta bukaci a kama shi sannan a gabatar da shi a gaban kotu ranar 16 ga watan Maris na 2020.

    ICPC na zargin Abdullahi Dikko Inde da laifin almundahana

    Asalin hoton, Facebook

  16. 'Yan damfara sun shiga ofishin mataimakin shugaban kasa

    Mataimakin shugaban kasar Kenya William Ruto ya yarda cewa "'yan damfara" sun ziyarci ofishinsa, wanda aka fi sani da suna Harambee House Annex.

    Ya kara da cewa 'yan jaridar da basu da aikin yi ne suka mayar da hankali a kansa, sannan ya dage cewa ofishinsa bai karbi kwangilar sayo wa gwamnati makamai ba.

    Amma kafofin watsa labaran Kenyan sun ce sakon da ya wallafa a Twitter tamkar amincewa ne cewa ministan harkokin wasanni Rashid Echesa, wanda ake zargi da shigo da makamai ta haramtacciyar hanya, ya yi amfani da ofishin mataimakin shugaban kasar wajen gudanar da kasuwancin makaman.

    A wani sakon Twitter da ya walafa, Mr Ruto ya bayyana Mr Echesa da wasu a matsayin "'yan damfara", bayan an wallafa rahoton da ya zargi Mr Echesa da yin amfani da Harambee House Annex wajen yin taruka.

    Mr Ruto, wanda aka kai samame a ofishinsa a karshen makon jiya kan wani bincike, ya ce bai taba haduwa da tsohon ministan ba, sannan kuma 'yan kasuwar da yake kai wa ziyara ba sa cikin wadanda ake zargi da hannu a badakalar da ta kai ta $397m.

    Shi ma Mr Echesa ya musanta zargin.

    Mr Ruto

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Mr Ruto ya musanta zargin
  17. Za a fara mayar da 'yan gudun hijirar da suka tsere Borno

    Bayanan sautiLatsa alamar lasifika domin sauraron cikakken rahoton

    Gwamnatin jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya ta ce nan da wata biyu ne za ta fara mayar da ‘yan asalin jihar da suka tsere zuwa kasashe makwabta sakamakon rikicin Boko Haram.

    Matakin dai ya biyo bayan ziyarar da gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya kai jamhuriyar Nijar a karshen makon jiya.

    Akwai akalla ‘yan asalin jihar Borno dubu dari da ashirin da ke gudun hijira a jamhuriyar Nijar, kuma akwai wasu da suka tsere kasashen Chadi da Kamaru a matsayin 'yan gudun hijrar.

  18. Coci ta gargadi 'mazinata' a Zambia

    Coci-coci a Zambia sun yi kira ga 'yan kasar su yi aiki tukuru domin rage yawan sake-saken auren da ke faruwa a tsakanin ma'aurata.

    Cin amanar aure da shaye-shayen kayan maye da cin zarafi tsakanin ma'aurata da rashin haihuwa da wuri da kuma rashin samun shawarwari a kan aure na cikin manyan abubuwan da suka haddasa rabuwar auren mutum 20,000 bara a kasar.

    Mata ne suka fi neman a sake su, kuma yawancin masu kashe aurensu basu wuce tsakanin shekara 25 zuwa 45 ba.

    Wani rahoto da jaridar Zambia Daily ta gwamnatin kasar ta wallafa ya kara da cewa rashin samun goyon baya daga wurin maza da kuma kashe dare a shafukan sada zumunta sn taimaka wurin mutuwar aure.

    Shugaban rukunin cocin Independent Churches of Zambia, Reverend David Masupa, ya ce "Wadannan alkaluma abin kunya ne kuma sun saba da koyawar littafin Injila a kan aure wanda ya ce 'mutu ka raba'"

    Mata ne suka fi neman a sake su, kuma yawancin masu kashe aurensu basu wuce tsakanin shekara 25 zuwa 45 ba.

    Asalin hoton, Getty Images

  19. Yadda masu larurar kuturta ke rayuwa a Najeriya

    Bayanan sautiLatsa nan domin sauraron rahoton Zahraddeen Lawan kan halin da masu larurar kuturta ke fuskanta

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce sama da mutum miliyan bakwai ne a fadin duniya larurar kuturta ta shafa, yayin da wasu sama da miliyan hudu ke rayuwa da mummunar nakasar da take haifarwa.

    Masana sun ce cutar kuturta na haifar da nakasa ta dindindin ga fatar jiki da jijiyoyi da gabobi da kuma idanu, musamman ga mutanen da larurar ta riska amma suka ki zuwa asibiti a kan lokaci har ta ci karfinsu.

    Akasari dai masu larurar kuturtar kan buge da barace-barace a tituna saboda ba kasafai suke samun damar yin karatu da abin yi ba.

  20. Dahiru Bauchi ya kai wa Buhari ziyara

    Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Dahiru Bauchi, ya kai wa shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ziyara ranar Lahadi.

    Hotunan da mai taimaka wa shugaban kasar kan kafafen sadarwa na zamani, Bashir Ahmad, ya wallafa a shafinsa na Twitter sun nuna shugaban kasar da Sheikh Bauchi da dansa da ma wasu 'yan rakiyarsa a fadar Aso Villa da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

    Ko da yake ba a fadi dalilin kai ziyarar ba, amma malamin ya je fadar shugaban Najeriyar ne a yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da ta'azzara a sassan kasar.

    Malamin ya yi shuhura wajen gaya wa shugabanni gaskiya.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X