Hukumar dakile yaduwar
cututtuka a Najeriya ta ce ta bude wasu dakunan gwaje-gwaje guda biyar don gano
tare da tantance masu dauke da utar zazzabin Lassa a kasar.
Babban Daraktan hukumar, Dakta
Chikwe Ihekweazu wanda ya bayyana hakan ranar Litinin a Abuja, babban birnin
kasar y ace an bude dakunan gwajin a wasu asibitoci da ke Edo da Ondo da Ebonyi
da Legas da kuma guda a harabar hukumar ta NCDC a Abuja.
Ihekweazu ya ce “a yanzu haka,
ana gwajin samfurin cutar da aka samo daga wasu masu dauke da cutar a jihohin
Kudu maso Kudancin kasar da kuma wasu jihohin Kudu maso yammacin kasar a
asibitin kwararru na Irrua yayin da ake gwajin samfurin cutar da aka samu daga
jihohin Kudu maso Yamma a asibitin koyarwa na Alex Ekueme da ke Abakaliki.
“Wadanda kuma aka samu daga
jihohin da ke arewacin kasar ana gwajinsu a cibiyar gwaje-gwaje ta NCDC a Abuja
sannan kuma samfurin cutar daga yankin Kudu maso Yamma ake gwajinsu a asibitin
koyarwa na jami’ar Legas yayin da sabon dakin gwajin da aka bude a cibiyar kula
da lafiya ta tarayya a Owo da ke Ondo ta ke karbar samfurin cutar na jihar Ondo
kadai.”
Shugaban hukumar NCDC ya ce
dakunan gwaje-gwajen wadanda aka gina kowane daya akan kudi naira miliyan 100
zasu taimaka wajen gano masu dauke da cutar ta Lassa a kasar.
A cewarsa, an samar da matakan
saukaka jigilar samfurin cutar daga jihohi zuwa wuraren gwaje-gwajen.
Ya kuma ce hakan zai rage
tsawon lokacin da ake shafewa kafin gano cutar da kuma tabbatar da ita wanda
hakan na iya rage yawan mace-mace sanadiyyar cutar.
Ihekweazu ya ce Najeriya tana
bada gudummawa ta fannin nazari da kuma bincike don gano rigakafin cutar ta
Lassa.
Ya kara da cewa dakunan
gwaje-gwajen zasu taka muhimmiyar rawa wajen wani bincike da za a gudanar kan
Lassa Fever wanda za a fara a karshen watan Maris.
A hannu guda kuma, mutane 25 ne
ya zuwa yanzu suka mutu sakamakon fama da zazzabi yayin da aka killace wasu
sama da 100 a wasu cibiyoyin kula da masu Lassa a sassan kasar.