Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da suka faru ranar Juma'a

Shafin da ke kawo labaran abubwan da ke faruwa kai tsaye a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da Chadi da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Sagiru Kano Saleh and Halima Umar Saleh

  1. Cutar pneumonia ka iya kashe yara fiye da miliyan daya a Najeriya - Unicef

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce kimanin yara miliyan da dubu dari hudu ka iya mutuwa a shekaru 10 masu zuwa sakamakon cutar sanyin huhu, wato pneumonia.

    Hukumar kula da kananan yara ta Majalisar, Unicef ce ta yi wannan hasashen inda take fadin cewa Najeriya ka iya zama kasar da tafi yawan mutuwa sakamakon cutar ta pneumonia.

    Bisa kididdigar da ta Unicef ta yi ta ce ta gano yara milyan 6.3 ka iya mutuwa saboda cutar numfashin a fadin duniya.

    Unicef ta ce ta gano kasar India ce za ta iya kasancewa ta biyu wajen cutar numfashi ga kananan yara, inda kuma jamhuriyar dimokradiyyar Congo ke biye mata baya a matsayi na uku.

    Hukumar ta Unicef ta yi gargadi ga hukumomi da su kara kaimi wajen kara yawan rigakafin cutar numfashin ta numoniya.

    To amma hukumar ta wallafa a shafinta na Twitter cewa Najeriya na yin irin wannan rigakafin.

  2. 'Yan majalisar Najeriya na son Buhari ya cire Hafsoshin tsaro

    'Yan majalisar wakilan Najeriya sun yi kira ga hafsoshin tsaron kasar da su yi murabus ko kuma Shugaba Buhari ya cire su.

    Sun yi wannan kira ne a zauren majalisar ranar Laraba,

    'Yan majalisar, yayin tattaunawa kan sha'anin tsaro sun ce hafsoshin tsaron katsar sun 'gaza samar da tsaron' da 'yan kasa ke muradi tun 2015 lokacin da Shugaba Buhari ya nada su a mukaman nasu.

    Hakazalika, su ma 'yan majalisar dattawan kasar sun yi kira ga Shugaba Buhari da ya gaggauta cire hafsoshin tsaron kasar da ya nada a watan Yulin 2015.

    Su ma sanatocin sun yi zargin cewa hafsoshin tsaron "ba su abin da aka nada su su yi ba", inda suka kara da cewa ba ma su da masaniyar abin da ya kamata a yi domin shawo kan matsalar tsaron da kasar ke bukata baya ga kasancewa a kujerun fiye da lokacin da tsarin mulki ya deba musu.

    Har wa yau, sanatocin sun yanke cewa Shugaba Buhari ya ayyana ta-baci kan harkar tsaro a kasar.

  3. Najeriya ta dauki matakin hana shigar cutar Coronavirus kasar

    Hukumomi a Najeriya sun ce sun fara daukar matakan ko-ta-kwana kan cutar Coronavirus.

    Dakta Abubakar Jafiya na cibiyar yaki da cututtuka a Najeriya ya shaida wa BBC cewa a shirye Najeriya take domin hana cutar shiga kasar.

    Ya kuma ce gwajin da Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi na matakin da Najeriya ta ke na hadarin kamuwa da cutar ba shi da yawa, don haka yiwuwar kamuwa da cutar a Najeriya ba shi da yawa.

  4. Mutum 15 sun mutu a harin 'yan tawaye a DRC

    Hukumomi a yankin gabashin kasar Demokaradiyar Kongo sun sanar da cewa akalla mutane 15 ne suka mutu.

    An dai yi ce wasu da ake zargin 'yan tawaye ne suka kashe su.

    Wannan kisa dai ya kasance na baya –bayan nan a cikin jerin hare –haren da ake kai wa da kuma ake gani ‘yan tawaye mambobin kungiyar Allied Democratic Forces ko kuma ADF ne ke kaiwa kan jama'a a kasar.

    Dakarun gwamnatin kasar Kongo dai sun ce su ma sun kai farmaki ga gungun 'yan tawayen tun cikin watan Oktoban shekarar da ta gabata.

  5. Batun tsige Donald Trump na ci gaba da tayar da kura

    Lauyan tsohon mai ba da shawara kan harkokin tsaro a Amurka, John Bolton, ya yi watsi da zargin fadar White House na cewa sabon littafinsa na dauke da bayanan sirri da dole sai an cire kafin a buga littafin.

    Lauyan ya ce babu wani abu a cikin babin da ya shafi Ukraine da za a kira bayanin sirri.

    Wasu bangarori na littafin da aka samu na zargin cewa Donald Trump ya fada wa Mista Bolton baki da baki cewa, ya dakatar da bai wa Ukraine agaji har sai gwamnatinta ta amince ta binciki abokin hamayyar Mista Trump, Joe Biden.

    Wannan dai shi ne babban lamari a batun tsige Mista Trump da 'yan jam'iyyar Democrat suka assasa.

  6. 'Yan sanda a Mexico na neman abokin burmin El Chapo

    'Yan sanda a Mexico sun kaddamar da bincike don gano wani shugaban gungun mashaya mafi girma a kasar, wanda ya tsere tare da wasu mutum biyu daga wani gidan yari mai tsananin tsaro.

    An tura 'yan sanda na musamman zuwa Mexico City tare da jirage masu saukar ungulu don nemo Victor Felix Beltran, wanda ke da dangantaka da tsohon shugaban kungiyar Sinaloa wato Joaquin Guzman wanda kuma aka fi sani da El Chapo.

    Tserewar Mista Beltran abin kunya ne ga hukumomin Mexico saboda Amurka ya bukaci a koma da mutanen uku.

    Wani jami'in gwamnati ya ce ma'aikatan gidan yarin ne suka taimaka masu suka tsere.

  7. 'Cutar coronavirus na kara yaduwa a duniya'

    Gwamnati China ta ce akalla mutane 170 ne kawo yanzu aka tabbatar cutar Coronavirus ta kashe, inda wasu mutane sama da 1700 suka sake kamuwa da ita.

    Yayin da ake ci gaba da kokarin dakile yaduwar cutar a fadin duniya, Hukumar Lafiya ta kasar China ta ce baki daya, mutum 7000 ne aka tabbatar sun kamu da cutar, kuma ana zargin wasu dubbai suna dauke da cutar.

    Hukumar Lafiya ta Duniya za ta yi taro a yau Alhamis don yanke shawara kan matsayin cutar ga kiwon lafiya a duniya.

    Wani jami'in hukumar Lafiya ta DUniya, WHO, Tedros Adhanom ya ce "yadda cutar ke kara yaduwa da kuma yadda ake iya daukar ta daga 'yan China ya matukar tayar da hankali.

    Duk da cewa yawan mutanen da suka kamu da ita a wajen China ba su da yawa." Hukumar ta ce ya kamata gaba daya duniya a dauki matakin dakatar da yaduwar cutar da ta samo asali daga birnin Wuhan na China.

    A wani bangaren kuwa An samu tsaikon tashi da saukar jiragen saman da za su kwaso mutane daga birnin Wuhan.

    Gwamnatocin sun yi shatar jiragen ne don debo 'yan kasarsu daga birnin, a lokacin da yawan mutanen da ke kamuwa da cutar ta Corona ke karuwa.

  8. 'Kira ga Buhari ya yi murabus ya saba da tinanin 'yan Najeriya'

    Fadar gwamnatin Najeriya ta bayyana kiran da wani sanata ya yi ga Shugaba Muhammadu Buhari ya yi murabus daga kujerar shugabancin kasar da ‘shirme’.

    Mai Magana da yawun shugaba Buhari, Malam Garba Shehu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

    A ranar Larabar ne dai Sanata Eyinnaya Abaribe ya yi kira ga Shugaba Buhari da ya hakura da kujerar shugabancin Najeriya ya sauka bisa zargin ‘gazawa a sha’anin tsaron kasar’.

    To sai dai sanarwar da Garba Shehu ya fitar ta ce kiran da Sanata Abaribe ya yi sam bai dace ba kuma ya saba da ra’ayin ‘yan Najeriya wadanda suka zabi Buhari a karo na biyu.

  9. Farawa

    Masu bibiyarmu barkanku da warhaka. Barkanmu da sake saduwa a yau Alhamis domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a Najeriya da makwabta da ma sassan duniya. Da fatan za ku kasance da shafin na BBC Hausa.com.

  10. Karshe

    Jama'a nan muka kawo karshen rahotonnin kai-tsaye. Mu hadu gobe Alhamis.

    Kafin nan, ku duba kasa domin karanta labaran yau.

  11. Gwamnan Borno ya nada Ibo da Bayarabe mukami

    Gwamnan Borno Babagana Umara Zulum ya rantsar da wasu mutane biyu da suka hadar da kabilar Igbo da wani Bayerabe a matsayin masu ba shi shawara na musamman.

    Cikin wata sanarwar kakakin gwamnan, Isa Gusau, ya ce yau Laraba ne gwamnan ya rantsar da Chief Kesta Ogualili daga jihar Anambra da kuma Alhaji Yusuf Alao daga jihar Oyo da wasu karin mutane ashirin da hudu.

    ''Sun kwashe tsawon shekaru a jihar ta Borno, kana sun taka muhimmiyar rawa a siyasar jam'iyyar APC a jihar'', inji sanarwar.

    Da yake rantsar da su a matsayin da aka ba su, mataimakin gwamnan jihar Umar Kadafur da ya wakilci gwamna Zulum, ya bukace su da su zage dantse domin ciyar da jihar gaba.

    Dukkaninsu sun yi alkawarin yin aiki tukuru domin tabbatar da nasarar jam'iyyar APC da kuma gwamnatin jihar.

  12. Kotu ta wanke Omo-Agege daga zargin aikata laifi a Amurka

    Wata babbar kotun tarayya a Abujan Najeriya ta kori karar da aka shigar gabanta domin ta sauke mataimakin shugaban Majalisar Dattawa Ovie Omo-Agege daga mukaminsa bisa zargin cewa wata kotu ta taba yanke masa hukunci a Amurka.

    A shari'ar ta yau Laraba, kamfanin dillancin labarai na NAN ya rawaito Mai Shari'a Othman Musa yana cewa karar bata lokacin kotu ne kawai domin kuwa babu wata kotu da ta taba daure shi a Amurka kuma ba ya fuskantar wata shari'a a kasar.

    Mai shari'ar ya umarci wanda ya shigar da karar da ya biya Omo-Agege kudi naira miliyan 1 sakamakon bata masa suna.

  13. Labarai da dumi-dumi, Arsenal ta dauki Pablo Mari

    Kungiyar kwallon kafar Arsenal ta sanar da daukar dan wasan bayan Sifaniya Pablo Mari a matsayin aro.

    Dan wasan mai shekara 26 na murza leda a Flamengo, inda ya taimaka wa kungiyar wurin lashe gasar Serie A ta Brazil da kofin Libertadores a bara.

    Ya taka wa Flamengo leda har sau 22 bayan komawarsa kungiyar a Yulin 2016 daga Manchester United.

    da ma dai ana sa ran kungiyar za ta dauki dan baya duba da irin matsalar da take fama da ita a bakin ragarta a kasuwar saye da musayar 'yan wasa ta watan Janairu.

  14. An bukaci Buhari ya yi murabus kan matsalar tsaro

    Shugaban marasa rinjaye na Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Enyinnaya Abaribe, ya bukaci Shugaba Muhammadu Buhari da ya yi murabus daga mukaminsa sakamakon rashin tsaron da ya adddabi kasar a baya-bayan nan.

    Sanatan yana wannan magana ne a zauren majalisar ranar Laraba yayin da 'yan majalisar ke tafka muhawara kan wani kudirin tsaro da Sanata Yahaya Abdullahi ya gabatar tare da goyon bayan sanatoci 105.

    "Muhimmin aikin da ya kamata a yi a Najeriya ba a yi shi ba. Muna neman wannan gwamnati ta yi murabus saboda babu abin da za ta iya yi a kasar nan," in ji Sanata Abaribe.

    Kudirin na Sanata Yahaya Abdullahi, wanda ya samu goyon bayan sanatoci 105, ya bukaci gwamnatin tarayya ta sanya dokar ta-baci kan harkar tsaro a kasa baki daya sannan kuma a kafa wani kwamiti na musamman da zai yi aiki da jami'an tsaro sannan ya bayar da rahotonsa ga Majalisar Dattijai.

  15. An gano hanyar da 'yan bindigar arewacin Najeriya ke samun makamai

    Wani bincike da aka gudanar ya bankado cewa makaman da ake amfani da su a tashe-tashen hankula a jihohi uku na arewacin Najeriya sun fito ne daga kasashen Libya da Turkiyya da kuma Ivory Coast.

    A cikin shekara uku, masu binciken daga cibiyar Conflict Armament Research sun tantance daruruwan bindigogi a jihohin Kaduna da Katsina da kuma Zamfara a Najeriyar, inda aka fi samun tashin hankali a-kai-a-kai tsakanin manoma da makiyaya.

    Sun gano wasu makamai da aka kera a kasar Turkiyya da ke da alaka da wani mutum da ba a bayyana sunansa ba.

    Kazalika sun gano wasu kananan bindigogi (assault rifles) daga kasar Iraki irin wadanda masu ikirarin jihadi suke amfani da su a yankin Sahel.

    Wasu daga cikin makaman sun fito ne kai-tsaye daga rumbun makaman gwamnatin kasashen.

    Kamanceceniya tsakanin makaman sun nuna cewa daga wuri daya ake samo su, sai dai cibiyar ta nanata cewa ba ta nufin 'yan bindigar da ke kashe mutane a arewacin Najeriya suna da alaka da kungiyoyin ta'addanci.

  16. Shaguna na ci da wuta a Kasuwar Balogun ta Legas

    Wani rukunin shaguna da ke cikin Kasuwar Balogun a birnin Ikkon Najeriya ya kama da wuta.

    Daya daga cikin abokan aikinmu na sashen Yarbanci a Legas ya ce ya hango tarnakin hayakin da ke tashi daga inda yake a CMS.

    Tuni 'yan kasuwa suka shiga halin rudu da rikicewar faruwar lamarin.

    Za mu kawo muku karin bayan nan gaba kada.

  17. Kasashen da ke kwashe jama'arsu daga China saboda Coronavirus

    Birnin Wuhan na yankin Hubei da ke kasar China ne hedikwatar annobar cutar numfashi ta coronavirus.

    Yankin na Hubei, wanda yanzu haka yake garkame (ba shiga ba fita), yana da mazauna mutum kusan milyan 60.

    Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito kasashen da suke kwashe jama'arsu daga yankin kamar haka:

    • Faransa
    • Koriya ta Kudu
    • Kazakhstan
    • Jamus
    • Morocco
    • Sifaniya
    • Amurka
    • Birtaniya
    • Rasha
  18. Gobara ta tashi a Kasuwar Balogun a Lagos

    Wani rukunin shaguna da ke cikin Kasuwar Balogun a birnin Ikkon Najeriya ya kama da wuta.

    Daya daga cikin abokan aikinmu na sashen Yarbanci a Legas ya ce ya hango tarnakin hayakin da ke tashi daga inda yake a CMS.

    Tuni 'yan kasuwa suka shiga halin rudu da rikicewar faruwar lamarin.

    Za mu kawo muku karin bayan nan gaba kada.

  19. Lassa ta kashe mutum 41 a Najeriya

    A kalla mutum 41 ne suka mutu sakamakon cutar Lassa a sassan Najeriya tun farkon shiga shekarar nan ta 2020 a cewar gwamnatin kasar.

    Ministan lafiya na kasar, Osagie Ehanire ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Abuja, babban birnin kasar.

    Kazalika Cibiyar hana yaduwar cututtuka ta kasar ma CDC ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar a shafinta na intanet.

    Ministan wanda ya yi karin haske kan cutar ta Lassa da ke ci gaba da yaduwa a kasar ya bayyana cewa kimanin jami'an lafiya biyu na daga cikin mutum 41 da suka mutu.

    Ehanihere ya kuma ce akwai mutum 258 da suka kamu da cutar daga sassan jihohin kasar 19.

    A cewar ministan lafiyar, ya kamata mutane su rika kula wajen tsaftace muhallinsu tare da kiallce abincinsu daga fadawa tarkon beraye.

    Game da cutar coronavirus kuwa, Ehanire ya ce akwai barazana sosai saboda yadda ake shigo da kayayyaki amma ya ce Najeriya ta tanadi matakan kariya musamman a tashoshin jiragen sama na kasa da kasa guda biyar.

    Kawo yanzu, ba a samu rahoton bullar cutar coronavirus ba a Najeriya duk da cewa Ivory Coast da Kenya suna sa ido kan wasu mutane da shiga kasashen daga China a baya-bayannan.

  20. An rufe wani babban kanti a Abuja saboda Coronovirus

    Rahotanni daga Abuja, babban birnin Najeriya na cewa gwamnati ta rufe wani babban kanti a unguwar Jabi bisa zargin shigo da dabbobi da nama dangin ruwa ba bisa ka'ida ba daga China - kasar da aka samu barkewar cutar Coronavirus mai yaduwa.

    Hukumar kare hakkin masu sayayya FCCPC a kasar ce ta dauki matakin rufe kantin ranar Laraba kamar yadda ta wallafa a shafinta na Twitter.

    Ta ce ta dauki matakin ne bayan wani samame sakamakon samun bayanai cewa kantin ya rufe saboda gudun abin da ka je ya zo game da cutar Coronavirus.