Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da suka faru ranar Juma'a

Shafin da ke kawo labaran abubwan da ke faruwa kai tsaye a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da Chadi da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Sagiru Kano Saleh and Halima Umar Saleh

  1. Masallacin Zahir da ke Kedah a Malaysia

    Masallacin Zahir, shi ne masallacin jihar Kedah, wanda ke kasar Malaysia, wanda ke tsakiyar garin Alor Star.

    An gina masallacin a shekarar 1912, da tallafin Tunku Mahmud, dan Sultan Tajuddin Mukarram Shah.

    Wannan masallaci babba ne sosai kuma yana da kayan kawa na zamani.

    Yana daga cikin manyan masallatai 10 mafiya kyau a duniya

  2. Farawa da rahotanni da labarai na ranar Juma'a 31 ga watan Janairun 2020

    Masu bin mu a wannan shafi assalamu alaikum barkanmu da safiya. Tare da yi muku barka da Juma'a.

    Halima Umar Saleh da Sagir Kano Saleh ne za su fara kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da sauran sassan duniya a yau Juma'a.

    Sai ku kasance tare da mu don jin abubuwan da ke faruwa, sannan kuna iya bin mu a shafukanmu na Facebook da Twitter da Instagram.

  3. Rufewa

    Jama'a a nan kuma muka kawo karshen labarun kai tsaye daga nan sashen Hausa na BBC - BBCHAUSA.COM.

    Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu. Usman Minjibir da Sagir Kano Saleh ke maku fatan mu kwana lafiya.

    Ku duba kasa domin ganin abubuwan da suka faru a yau Alhamis.

    Gobe idan Allah Ya kai mu za mu ci gaba da kawo maku karin wasu labaran.

  4. Sojojin Amurka ba za su bar Afirka ba - Esper

    Amurka ta ce ba za ta janye dakarunta daga nahiyar Afirka ba.

    Sakataren tsaron Amurka Mark Esper ya bayyana haka a yau Alhamis yayin da yake bitar ayyukan dakarun kasar da nufin samun karin kaimi domin tunkarar barazanar China.

    ''Ba za mu janye duka dakarunmu daga Afirka ba... na san hakan na damun da dama amma ina so in tabbatar masu cewa ba a dauki matsayi a kan hakan ba,'' inji Esper.

  5. Sojoji sun kashe mahara 21 a Chadi

    Sojojin Chadi sun kashe mahara 21 a wani hari da masu ikirarin jihadi suka kai masu a yau Alhamis.

    Shugaban rundunar sojin kasar ya ce an kashe mayakan ne a kwanton baunar da suka yi wa sansanin sojoji masu aikin kawar da ragowar 'yan kungiyar Boko Haram da suka tsere a yankin tabkin Chadi.

    Janar Taher Erda ya ce soja uku da wata farar hula sun mutu a harin tsibiri da ke iyaka da Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi.

    A shekarar 2009 kungiyar Boko Haram ta fara kai hare-hare a makwabtan Chadi.

    A 2016 wani yanki ya balle da kungiyar inda ya yi mubaya'a ga kungiyar ISWAP wanda bangare ne na kungiyar IS.

    Kungiyar ISWAP ta addabi yankin kasashen Benin da Kamaru da Nijar da Chadi da Najeriya, wadanda suka kafa rundunar hadin gwiwa domin yakar ayyukan masu ikirarin jihadi.

    A farkon watan Janairun nan da muke ciki ne Chadi ta janye sojanta 1,200 na rundunar daga Najeriya zuwa yankin tabkin Chadi bisa hujjar karewar wa'adin aikin rundunar.

    A ranar Litinin din makon da muke ciki an kashe sojan Chadi shida a wani kwanton baunar da aka yi wa sansaninsu a Tetewa. A makon jiya ma sai da wani dan kunar bakin waki ya kashe fararen hula tara a yankin.

    Bayan nan a jiya Laraba wasu da ake zargi 'yan kungiyar Boko Haram ne sun kashe mutum biyar a wani kauye da ke arewacin Kamaru.

  6. An sallami ma'aikata 5,000 a Adamawa, An dauke su aiki tsakanin shekarar 2018 zuwa 2019

    An sallami ma'aikata 5,000 a jihar Adamawa a yankin arewa masu gabashin Najeriya.

    Gwamnatin jihar ta sanar da sallamar ma'aikatan ne bayan majalisar zartsawar jihar ta amince da shawarwarin da kwamitinta kan daidaita tsarin daukar ma'aikata ya bayar kan lamarin.

    Kakakin gwamnatin jihar Umar Garba Pella ya shaida wa BBC cewa ma'aikatan da sallamar ta shafa su ne wadanda aka dauka aiki ba bisa ka'ida ba tsakanin watan Nuwamban shekarar 2018 da watan Mayun shekarar 2019.

    Don haka gwamnatin ta ce wadanda dakatarwar ta shafa sai sun sake neman a dauke su aiki.

  7. Za a rufe sansanin 'yan gudun hijiran MDD a Libya

    Hukumar 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta dakatar da ayyuka a cibiyarta da ke Tripoli babban birnin kasar Libya saboda dalilan tsaro.

    Sanarwar da hukumar ta fitar ya biyo bayan ci gaba da samun rikici tsakanin bangarori masu yaki da juna a kasar duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da suka kulla a watan Afrilu.

    Hukumar tana amfani da cibiyar ne wurin ajiy masu neman mafaka da 'yan gudun hijira zuwa wasu kasashe karkashin ma'aikatar cikin gida ta Libya.

    Matakin rufe cibiyar na wucin gadi ya biyo bayan atisayen da 'yan sanda da sojoji ke yi a kusa da gidajen da cibiyar ke amfani da su.

    Tana kuma tsoron sansanin na iya fuskantar barazanar kawo hari sakamakon rikicin na Tripoli.

    Daruruwan mutane ne dai ake sa ran mayar da su zuwa wasu sassan birnin inda za su samu tallafin kudade da magunguna da sauransu.

  8. Yadda za a yi da wadanda za su shigo daga China

    An bukaci hukumar kula da sufurin jiragen sama a Najeriya ta yi cikakken tantancewa a kan wandan suka dawo daga kasar Chana domin dakile yiwuwar yaduwar cutar Coronavirus.

    Majalisar dattawan kasar ta kuma bukaci 'yan China da suka je halarci bikin sabuwar shekarar China da su killace kansu a gidaje kuma su guji shiga cikin mutane na akalla makonni biyu.

    'Yan majalisun sun kuma shawarci masu niyyar yin tafiye-tafiye zuwa China su dakata har sai an magance cutar.

    Zaman majalisar ya bayyana bukatar gwamnatin kasar ta bayar da ba wa hukumar hana yaduwar cututtuka isassun kudade domin samun kayan aiki na zamani da suka dace domin daukar mataki kan annobar da ta yi ajalin mutane da dama a China.

  9. Rasha ta rufe iyakarta da China saboda coronavirus

    Rasha ta ba da umarnin rufe iyakarta mai tsawon kilomita 4,000 da makwabciyarta China inda aka fara samun annobar coronavirus.

    Mutane dari da saba'in da bakwai ne suka mutu sakamakon cutar bayan wasu dubu takwas da suka kamu da ita.

    Hukumar lafiya ta Duniya tana ganawa don yanke hukunci ko za a ayyana dokar ta-baci a duniya game da cutar.

    John Oxford, wanda farfesa ne a sashen nazarin kwayoyin cuta a Jami'ar London, ya shaida wa BBC cewa ba yanzu ya kamata WHO ta yanke shawara kai tsaye ba.

    ''Muna tattaunawa ne kawai da wasu kwayoyin cuta ne a duniya don haka ina ganin yadda abin yake da tsaurin yanke shawara kan makoma ko kuma tasirin kwayoyin cutar da kuma barazanarta'', a cewarsa.

    A nata bangaren, China ta bukaci manoma su ci gaba da samar da abinci bayan rahotannin hauhawar farashin kaya da karancin abinci yayin da kasar ke yaki da cutar coronavirus.

    Hukumomi sun ba da umarnin a bar hanyoyi a bude domin manyan motocin da ke shigo da abinci ga dubban mutanen da ke killace a lardin Hubei, inda aka samu barkewar annobar.

    Kasashe masu makwabtaka da China sun fara rufe hanyoyin da suka hada su da China.

  10. Za a soke karin tashin jiragen sama a Afirka ta Kudu

    Kamfanin jirgin saman Afirka ta Kudu SAA zai kara soke wasu tafiye-tafiyen jiragensa a kokarin kamfanin na inganta ayyukansa.

    A yau Alhamis ne kjamfanin ya sanar da soke tashin gomman jiragensa nan da watanni masu zuwa saboda karancin ciniki gabanin watan Fabrairu mai zuwa.

    A farkon wannna makon ne kamfanin ya ce zai karbi tallafin dala miliyan 235 daga bankin kula da ci gaban kasar.

    Sama da mako guda da ya wuce kamfanin ya soke tashin jiragensa sau 30 a yunkurinsa na rage kashe kudade.

    Tun a watan Disamban shekarar 2019 ne aka fara ba wa kamfanin kariya daga durkushewa.

  11. Da sauran rina a kaba a rikicin kogin Nilu

    An kasa cimma matsaya a takaddamar da ake yi a kan kogin Nilu da ya ki ci ya ki cinyewa tsakanin Masar da Sunan a Amurka.

    Ana ci gaba da tattaunawar da ta kunshi gina tashar wutar lantarki mafi girma a Afirka bayan cikar wa'adin da aka sa da farko ya kare a jiya Laraba. Amurka da bankin duniya ne ke jagorantar sasancin.

    Sai dai an kasa cimma matsaya a kan yadda madatsar ruwar da darajarta ya kai dala biliyan 4 za ta rika aiki.

    Kazalika ba a cimma daidaito ba kan yawan ruwan da madatsar za ta rika adanawa ba da kuma wanda za ta rika turawa daga Habasha.

    Masar na bukatar ba ta tabbaci game da yadda ya za magance matsalar karancin ruwa idan tashar ta fara aiki nan gaba a cikin wanann shekarar.

  12. Shugaba Buhari ya sake gana wa da Jonathan

    Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya gana da tsohon shugaban kasar, Goodluck Ebele Jonathan, a fadar gwamnati da ke Abuja yau Alhamis.

    Mai magana da yawun shugaba Buhari, Femi Adesina ya wallafa hotunan ganawar shugabannin biyu.

    Sai dai Femi Adesina bai yi bayani ba kan hakikanin abin da shugabannin guda biyu suka tattauna a yayin ziyarar.

    Shugaba Buhari ya gana da tsohon shugaban kasar ne daidai lokacin da wasu 'yan majalisar dokokin kasar suka yi kira a gare shi ya sauka daga mulki saboda tabarbarewar harkokin tsaron kasar.

    Wannan ne dai karo na biyu da tsohon shugaban ke ziyarta shugaba Buhari a baya-bayan nan.

  13. An rantsar da sabbin 'yan majalisa

    Sabbin 'yan majalisar wakilai sun fara aiki a Najeiya.

    Shugaban majalisar Femi Gbajabiamila ya ba wa sabbin 'yan majalisar rantsuwarsu ta kama aiki ne a lokacin zaman majalisar na yau Alhamis.

    Wadanda aka rantsar din su ne Abubakar Abdullahi Ahmed daga jihar Soko da Kolapo Osunsanya daga jihar Ogun.

    Sauran su ne Jerry Alagbaoso daga jihar Imo da kuma Nsikak Ekong daga jihar Akwa Ibom.

  14. CBN: Majalisa ta amince da nadin Obiora

    Nadin Kingsley Isitua Obiora a matsayin mataimakin gwamanan babban bankin Najeriya CBN ya samu amincewar majalisar dattawan kasar.

    Bukatar hakan da shugaba Buhari ya mika mata ne bayan karbar rahoton kwamitinta na ayyukan banki da inshora da kamfanonin hada-hadar kudi.

  15. Majalisa ta amince da nadin sabon shugaban hukumar alhazan Najeriya

    Majalisar dattawan Najeriya ta amince da nadin Zikrullah (Sikiru) Olakunle Hassan a matsayin sabon shugaban hukumar alhazai NAHCON.

    Majalisar ta amince da nadin ne bayan karbar rahoton kwamitinta kan harkokin waje game da bukatar hakan da Shugaba Muhammadu Buhari ya mika ta neman amincewa da nadin Zikrullah da sauran shugabannin hukumar.

    A zamanta na ranar Alhamis, majalisar ta kuma amince da nadin Abdullahi Magaji Hardawa a matsayin babban kwamishinan hukumar.

    Sauran manyan kwamishinonin hukumar su ne Nura Hassan Yakasai da Sheikh Momoh Suleman Imonikhe da Abba Jatois da Halima Jibril da Garba Umar da Ibrahim Ogbonnia Amah da sauransu.

  16. Aikin soji: Za a dauki mutum 10,000 a Mali

    A kokarinta na yakar matsalar tsaro da hare-haren masu ikirarin jihadi a kasar, gwamnatin Mali za ta dauki karin sojoji 10,000 aiki.

    Firai minista Boubou Cisse ya ce za a dauki karin sojojin ne nan da 'yan watanni masu zuwa, a kasar da ake hasashen yawan dakarunta bai haura 20,000 ba.

    A kwanakin baya masu ikirarin jihadi masu alaka da kungiyar Al-ka'ida sun kashe gomman sojojin kasar.

    A karshen makon da ya wuce kuma sojojin kasar 20 sun mutu a wani hari da aka kai wa sansanin sojojin.

    Ana ci gaba da samun tashe-tahen hankula a kasar inda sojojin Faransa ke taimakawa wajen samar da tsaro.

  17. Kotu ta bayar da belin Adoke kan Naira milyan 50

    Wata babbar kotu a Abuja ta bayar da belin tsohon ministan shari'ar Najeriya Mohammed Bello Adoke a kan naira miliyan 50.

    Gwamantin kasar na zargin Adoke da rashawar miliyan 300 a badakalar dala biliyan 1.3 na rijiyar mai ta Malabu a 2011. Sauran zargin sun hada da ta'ammuli da haramtattun kudade.

    Kotun ta kuma bukaci Adoke ya mika mata fasfonsa sannan ya kawo mutum daya da ya mallaki gida a Abuja da zai tsaya masa, wanda zai rika halartar zaman kotun tare da wanda ake zargin.

    Haka kuma mai shari'a Othman Musa ya bayar da belin Aliyu Abubakar da Rasky Gbinigie da ake zargi tare da Adoke a kan naira miliyan 50 kowannensu tare da sauran sharuddan da ta gindaya masa.

  18. Za a gina tituna da kudaden Abacha

    Gwamnatin Najeriya ta ce za ta kwato wasu karin dala miliyan 321 na iyalan tsohon shugaban kasar na mulki soja Sani Abacha daga kasashen waje.

    Minsitan shari'a Abubakar Malami ya ce gwamnati za ta yi amfani da kudaden iyalen Abachan da za a karbo wajen aikin gina manyan tituna kasar.

    Titunan sun hada da ta Lagos-Ibadan da Abuja-Kano da kuma gadar Second Niger.

    Malami ya ce gwamnatin na dab da rattaba hannu tsakaninta da tsibirin jersy inda aka taskace kudin da kuma Amurka kan yadda za a dawo wa Najeriya da kudaden nan ba da jimawa ba.

    Da yake jawabi ga 'yan jarida bayan taron majalisar zartaswar kasar, Malami ya ce gwamnati na tattaunawa da kasashe domin kwato karin wasu kadarorin da wasu tsoffin jami'an gwamantin kasar ake zargi da sata suka taskace a kasashen ketare.

    Wadanda za a kwace kadarorin daga hannunsu sun hada da tsohuwar ministar albarkatun mai Deizani Alison Madueke da tsoshon gwamnan jihar Delta James Ibori da Kola Aluko ake zargi da satar kudaden gwamnati, daga kasashen ketare.

  19. Labarai da dumi-dumi, Buhari na gana wa da hafsoshin tsaro

    Shugaba Muhammadu Buhari na ganawa da hafsoshin tsaron kasar a fadar gwamnati da ke Abuja.

    Jaridar The Nation ta rawaito cewa mutanen da suka hallara a wurin ganawar da ke gudana yanzu haka sun hada da sakataren gwamnati, Boss Mustapha da shugaban ma'aikata ga shugaban kasa, Abba Kyari da ministan tsaro Manjo Janar mai ritaya, Bashir Salihi Mahashi da ministan Harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola da kuma bai wa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro Babagana Monguno.

    Hafsoshin tsaron da suka hallara a wurin ganawar su ne hafsan hafsoshin kasar, Janar Gabriel Olonisakin da hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Tukur Buratai da hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Ibok Ekwe Ibas da hafsan sojin sama, Air Marshall Sadique Abubakar da kuma sifeto janar na 'yan sanda Mohammed Adamu.

    Sauran su ne darekta janar na hukumar leken asiri ta NIA, Ahmed Rufa’i Abubakar da darekta janar na hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, Yusuf Magaji Bichi.

    Babu wanda ya yi wa manema labarai karin bayani dangane da dalilin taron da aka fara da karfe 10 na safiyar Alhamis.

    Sai dai a kan iya alakanta shi da kiraye-kirayen da majalisun dokokin Najeriya suka yi ta yi a ranar Laraba kan tabarbarewar harkar tsaro a kasar, ciki da masu kira da a cire hafsoshin tsaron.

  20. 'Yar Bill Gates za ta auri dan Afirka

    'Yar attajirin nan mai asusun Bill and Melinda Gates, Jennifer, ta sanar da cewa an yi mata baiko da saurayinta dan kasar Masar, Nayel Nassar.

    Jennifer Gates da Nassar sun kwashe shekara uku suna soyayya, kuma sun sanar da baikon nasu ne yayin wasan zamiya da suke yi.

    Jennifer ta sanar da baikon nasu ne a shafinta na Instagram.