Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da suka faru a Najeriya da Nijar da duniya

Wannan shafin namu na kawo muku irin wainar da ake toyawa a Najeriya da Niger da Kamaru da Chadi da Ghana da sauran kasashen Afirka da ma fadin duniya.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Umar Rayyan

  1. Mutum 81,000 na dauke da kanjamau a jihar Delta - Amurka

    Gwamnatin Amurka ta ce akwai mutum kimanin 81,000 masu dauke da cutar kanjamau a jihar Delta da ke kudancin Najeriya.

    Akwai dai mutum milyan 1.9 da ke dauke da cutar a Najeriya.

    Amurkar ta nuna rashin jin dadinta kan irin kudin da masu asibitoci a jihar ke karba daga hannu masu dauke da cutar.

    Mataimakin jakadan ofishin jakadancin na AMurka a Najeriya, Kathleen FitzGibbon, ya bayyana damuwarsa ne ranar Alhamis lokacin da ya jagoranci wata tawaga yayin wata ziyara ga gwamnan jihar, ta Delta, Ifeanyi Okowa, bayan da jihar ta kaddamar da maganin cutar kanjamu da Amurka ta bayar da tallafinsa.

  2. 'Yan Niger na son kawo karshen hare-hare kan sojojinsu

    A jamhuriyar Nijar kwana daya da kai harin ta'adanci a sansanin soji mai nisa da ke Shinagodrar kan iyaka kasar Mali da ya yi sanadiyar mutuwar sojojin kasar 25 da mahara 63, 'yan kasar sun suka fara kira ga shugaban kasar Mahamadou Issoufou da ya dauki mataki na ayita ta kare.

    'Yan kasar sun ce sun gaji da yadda ake kashe masu sojoji.

    Sai dai yayin da ya rage kwanaki 3 a gudanar da taron da shugaban kasar Faransa ya kira shuwagabanin G5 Sahel kan zaman dakarun kasar ta Faransa a yankin Sahel, gwamnatin Nijar ta jinjina wa dakarun kasar na Faransa na Operation Barkhane da ta ce sun tallafa wa dakarun Nijar din wajen fatatakar maharan na Shinagodrar.

  3. Tambuwal ya ce jihar Sokoto za ta fara biyan albashin N30,000 a Janairu

    Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal ya bayar da umarnin fara biyan ma'aikatan jihar sabon albashi mafi karanci na naira 30,000 da watan Janairun 2020.

    Har wa yau, gwamna Tambuwal ya kuma bayar da umarnin gaggauta tantance ma'aikatan gaskiya da na boge domin tsaftace tsarin albashi.

    Gwamna Aminu Tambuwal ya bayar da umarnin ne a lokacin da ya karbi rahoton kwamitin da jihar ta kafa kan fara biyan albashin mafi karanci.

    Haka zalika, Gwamna Tambuwal ya sha alwashin biyan ma'aikata dukkannin hakkokinsu da aka samu tsaikon biya sakamakon shirin da gwamnatin jihar ta bullo da shi na tsaftace tsarin aikin gwamnati.

  4. 'Mutane ne ke gayyato masu garkuwa zuwa garuruwansu'

    Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ya yi zargin cewa wasu mutane a jihar sun rungumi wata halayya ta gayyatar masu garkuwa da mutane zuwa cikin gari domin sace jama'a.

    Gwamna Masari ya bayyana cewa mazauna garuruwan da ke kan iyakar Najeriya da Nijer ne suka fi yin wannan ta'ada musamman mutanen garin Jibiya.

    A wani bidiyo da ya yi hira da 'yan jaridu wanda kuma yake ta karakaina a shafukan sada zumunta, Gwamna Masari ba tare da kumbiya-kumbiya ba ya kama sunan mutanen Jibiya inda ya ce su ne ke kara lalata harkar tsaron garunsu da kansu.

    Daga karshe Masari ya jadda cewa shirin sasanci tsakanin gwamnati da al'umma da masu garkuwa da mutane da ke zaune a cikin daji na nan daram, inda ya ja hankalin masu cewa shirin ya wargatse.

    A ranar Larabar nan ne dai wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da wasu jami'an kwastam guda biyu a wani shinge da ke kauyen Dan-bedi a yankin karamar hukumar Jibiya ta jihar Katsina mai iyaka da jamhuriyar Nijer.

    Batun hare-hare da sace jama'a dai ya zama ruwan dare a jihar Katisna, inda da wuya rana ta fito ta fadi ba tare da samun wani gari ko kauyen da aka masu satar jama'a suka far wa ba.

    A cikin 2019 ne dai gwamnatin jihar ta Katsina ta bullo da shirin tattauna wa da masu garkuwa da jama'a da satar shanu.

  5. Ganawar Buhari da kungiyar ASUU ba a cimma matsaya ba

    Ganawar da shugaba Muhamadu Buhari ya yi da shugabannin kungiyar malaman jami'a wato ASUU dangane da shigar da su tsarin biyan albashi na bai daya, an tashi ba tare da cimma wata matsaya ba.

    Ganawar wadda aka yi ta da yammacin Alhamis an ce dukkanin bangarorin sun ki amince wa da bukatun juna.

    Sai dai shugaba Buhari ya nemi malaman na jami'o'i da su shiga tsarin biyan albashin na bai daya na IPPIS, domin ci gaban kasa.

    To amma an ce kungiyar ta ASUU ta tsaya kai da fata cewa shiga IPPIS ya saba da dokokin da suka kafa jami'o'i da kuma yarjejeniyar da kungiyar ta cimma da gwamnatin tarayya.

  6. Ministan Afirka ta Kudu ya bukaci halarta wiwi

    Ministan Kudin Afirka ta Kudu Tito Mboweni ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter cewa zai gabatar da wannan shawara ga gwamnati.

    Ya kuma wallafa wasu hotuna da ke nuna ganyen wiwin ya girma.

    A 2019, kotun kundin tsarin mulkin kasar Afirka ta Kudu ta halarta ajiyar tabar wiwi da yin amfani da ita har ma da shuka ta.

    Sayar da tabar wiwi ko ta wace fuska a kasar haramun ne.

  7. An sace dalibai a Kaduna

    Rundunar 'yan sanda a jihar Kaduna ta tabbatar da sace wasu dalibai hudu na Kwalejin addinin Kirista ta Good Shepherd Major Seminary School da ke garin Kakau a kan hanyar ta Abuja zuwa Kaduna.

    Jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan a jihar DSP Yakubu Sabo ya shaida wa BBC maharan sun shige daji da daliban.

    Har ila yau ya ce maharan sun fara magana da iyayen yaran.

  8. An fara binciken bidiyon ' 'yan sanda masu POS'

    Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kaddamar da bincike domin gano sahihancin wani hoton bidiyo da ya nuna yadda wasu jami’an ‘yan sanda ke amfani da na’urar cirar kudi ta POS wajen karbar cin hanci da ga jama’ar gari.

    Rundunar ta bukaci duk wani mai bayanai da ya taimaka su tuntube ta ta shafin pressforabuja@police.gov.ng

    Babban sufeton ‘yan sandan kasar ya yi tur da karbar cin hanci a tsakanin ma’aikatan gwamnati musamman ‘yan sanda.

    Ya kuma ce rundunar a shirye take ta hukunta duk wani jami’i da aka samu da hannu a cin hanci da rashawa.

  9. Buhari ya yi Alla-wadai da kisan Plateau

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da wani hari da wasu 'yan bindiga suka kai karamar Hukumar Mangu ta jihar Plateau, kamar yadda mai magana da yawun shugaban Malam Garba Shehu ya bayyana a shafinsa na Twitter.

    Maharan sun kashe mutum 12 da jikkata wani guda a kauyen Kulben, kamar yadda rundunar 'yan sandan kasar ta tabbatar.

    Ganau sun ce maharan sun yi wa kauyen dirar mikiya ne a daren ranar Laraba, inda suka rika yin harbi kan mai uwa da wabi.

    Daga nan wasu daga cikin mutanen kauyen suka tsere cikin daji don tsira da ransu.

    'Yan sanda sun ce an aike da jami'ansu can, amma ba a kama kowa ba tukuna.

    Sai dai Garba Shehu ya ce Shugaba Buhari ya fara magana da Gwamnan jihar Simon Lalong da sojoji da 'yan sanda da kuma sauran jami'an tsaro don binciken al'amarin da kuma kiyaye faruwarsa a gaba.

  10. An kashe sojoji 25 a Nijar

    Rundunar soji a jamhuriyar Nijar ta ce wasu da ake zargin ‘yan tada kayar baya ne sun kai hari wani sansanin soji, inda suka kashe kimanin sojoji 25.

    Harin na zuwa ne ‘yan kwanaki gabanin gudanar da wani taro don duba ayyukan sojoji a yankin Sahel da za a yi a kasar Faransa da shugabannin kasashen Afirka ta yamma.

    Harin ya faru ne kan wani sansanin soji da ke yammacin Nijar kusa da iyakar kasar da Mali.

    Wajen yana da kusanci da inda aka kashe sojoji 71 wata daya da ya gabata a wani hari da kungiyar ISIS ta dauki nauyin kai wa.

    Masu tada kayar baya da ke da alaka da kungiyar al-Qaeda suna gudanar da ayyukansu a yankin yayin da Boko Haram kuma suka fi karfi a kan iyakar kasar da ke kudu maso gabas.

    Rahotannin farko sun nuna cewa dakarun Faransa da takwaransu na Amurka sun kai dauki domin fatattakar masu tada kayar bayan.

    Mali da Burkina Faso da kuma Nijar sun shafe tsawon shekaru suna yaki da masu tada kayar baya, sai dai adadin hare-haren da ake kai wa ya karu matuka duk da dubban dakarun da aka jibge domin yaki da matsalar taro.

  11. Barka da shigowa wannan shafi inda za mu rika kawo muku labarai da bayanai kai-tsaye game da abubuwan da suke faruwa a Najeriya da Nijar da Ghana da kuma sauran sassan duniya.

  12. Karshe!

    Nan muka kawo karshen labarai da bayanai kai-tsaye da muke kawo maku a wannan shafi. Sai kuma gobe. Mun gode.

  13. Labarai da dumi-dumi, ICRC ta karbi mutum 10 da harin Monguno ya rutsa da su

    Kungiyar bayar da agaji ta ICRC ta bayyana cewa likitocinta sun karbi wadanda suka samu raunuka 10 daga harin da aka kai a garin Monguno na jihar Borno.

    A ranar Talata ne dai Kungiyar nan da ke ikirarin jihadi ta ISWAP ta bayyana cewa ta kai hari a garin Monguno inda ta ce ta kashe sojoji takwas.

    Sai dai wasu majiyoyi sun shaida cewa sojoji uku ne kawai suka kashe.

    Kungiyar ta ICRC ta bayyana a shafinta na Twitter cewa ta ceto marasa lafiyan biyar da mota biyar kuma da jirgi.

  14. Najeriya za ta karbi gasar kwallon mata ta Afirka

    Hukumar kwallon kafa ta Najeriya, NFF ta sanar da niyyar karbar bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka ta mata ta 2020.

    Domin karin bayani, ku shiga nan

  15. Karancin abinci da magunguna na 'kashe fursunoni'

    Akalla fursunoni 17 ne suka mutu a makon da ya gabata a babban gidan fursunan Jamhuriyyar Dimokradiyyar Congo, inji kungiyar Bill Clinton Foundation for Peace.

    Kungiyar ta shaida cewa yunwa da karancin magunguna ne musabbabin mutuwar fursunonin.

    Gidan fursunan Makala da ke Kinshasa babban birnin kasar na dauke da fursunoni sama da 8,000.

    Jami'an kasar sun bayyana cewa an shafe watanni biyu ba a kai kayan abinci gidan fursunan ba.

    Fursunonin sun dogara ne da iyalansu domin kawo musu abinci.

    Gidan fursunan ya cika makil, a yanzu haka gidan na dauke da fiye da abin da yakamata ya dauka na fursunoni sau biyar.

    An bayyana cewa abin ya yi tsanani inda kungiyoyi masu zaman kansu suka bayyana cewa akalla akwai fursunoni 100 da ke fama da matsananciyar rashin lafiya.

  16. Labarai da dumi-dumi, Jirgin Afirka ta Kudu ya yi saukar gaggawa a Congo

    Wani jirgin soji na Afirka ta Kudu ya yi saukar gaggawa a filin jirgin garin Goma da ke Jamhuriyyar Dimokradiyyar Congo, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

    An bayyana cewa jirgin na dauke da fasinjoji 58 da kuma ma'aikatan jirgi 8.

    Babu wani cikakken bayani dangane da abin da ya jawo saukar gaggawar sai dai an shaida cewa fiffiken jirgin na hagu ya kama da wuta yayin da jirgin ke sauka.

    Jami'an kashe gobara sun yi kokarin kashe wutar kuma sun ceto duka fasinjojin daga cikin jirgin.

    Jirgin ba mallakar aikin wanzar da zaman lafiya bane na Majalisar Dinkin Duniya bane sai dai jirgin yana taimaka wa wajen kai sojojin Afirka ta Kudun zuwa aikin wanzar da zaman lafiya a kasar ta Congo.

  17. EFCC ta kai samame gidajen Shehu Sani na Abuja

    Jami'an hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa EFCC sun kai samame a ranar Laraba gidajen Sanata Shehu Sani a Abuja.

    Domin karin bayani, ku shiga nan.

  18. 'Yan sanda sun kama mutumin da ke sayar wa barayin jama'a makamai

    'Yan sanda sun kama wani matashi da suke zargi da 'gawurta' wajen sayar da makamai ga masu garkuwa da mutane a yankin arewacin Najeriya.

    Rundunar 'yan sandan kasar dai ta ce ta kama mutumin ne a yankin jihar Niger.A wani faifan bidiyo da jaridar PRNigeria, ta ce ta samu , mutumin da ake zargin wanda ya yi magana da Hausa yayin tambayoyin da DSP Hassan Gimba Sule, jami'in 'yan sanda mai kula da ayyukan rundunar Special Tactical Squad a jihar Niger.

    Mutumin da ake zargin wanda haifaffen jihar Plateau ne ya ce ya kwashe shekaru fiye da uku yana sana'ar sayar da makamai ga bata gari.

    Ya kuma yi bayani cewa yana sayo bindigogi ne daga wani mutum a birnin Jos domin sayar wa masu garkuwa da fashi.

    Ya ce "ina sayen bindigogi kirar AK-47 da harsasai da kananan bindigogi, inda nake safarar su ga masu garkuwa da jama'a da 'yan fashi da ke jihohin Niger da Kaduna da Zamfara da Katsina da kuma Nassarawa.

    Ina sayen bindiga a kan naira 90,000 inda nake sayar da ita a kan naira 120,000."

    Wanda ake zargin wanda aka kama a Minna na jihar Neja an kama shi da kananan bindigogi guda biyu and harsashi 46.

  19. An kai harin roka kan sojojin Majalisar Dinkin Duniya a Mali

    Wani harin roka da aka kai kan wani sansanin sojan Majalisar Dinkin Duniya a Yankin Kidal da ke arewacin Mali ya jikkata mutum 20 da suka hada da sojojin Majalisar Dinkin Duniya masu wanzar da zaman lafiya guda 18, kamar yadda mai magana da yawun Majalisar Dinkin Duniya ya shaida wa BBC.

    Sojojin masu wanzar da zaman lafiya guda shida sun jikkata sosai sakamakon harin da aka kai da misalin karfe 6 na safe.

    Wannan na zuwa ne 'yan awanni bayan da jakadan Majalisar Dinkin Duniya a Afirka ta yamma da yankin Sahel, Mohammed Ibn Chambas ya ce yankin Afirka da Sahel na fuskantar karuwar hare-haren ta'addanci.

  20. 'Hare-hare na karuwa a Afirka ta yamma da yankin Sahel'

    Jakadan Majalisar Dinkin Duniya a Afirka ta yamma da yankin Sahel, Mohammed Ibn Chambas ya ce yankin ya fuskanci karuwar hare-haren ta'addanci a 'yan watannin baya.

    Ibn Chambas ya shaida wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa hare-haren sun kazanta a wannan shekara a dai-dai lokacin da kasashen yankin shida ke shirin shiga manyan zabukansu.

    Chambas ya ce hare-hare a Burkina Faso da Mali da Niger sun karu da kashi biyar tun 2016, inda aka samu rasa rayuka fiye da 4000 a 2019 kadai.

    Rashin tsaro dai na karuwa a yankin Sahel duk da dubban sojojin da ke jibge a yankin da suka hada da dakaru 4500 na Faransa da kuma dakarun wanzar da zaman lafiya 12000 na Majalisar Dinkin Duniya.