Abdelmajid Tabboune ne sabon shugaban Algeria

Wannan shafi zai rika kawo maku abin da ke faruwa kai-tsaye a Najeriya da Nijar da Ghana da kuma Kamaru, har ma da sauran kasashen Afirka masu makwabtaka.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Fauziyya Kabir Tukur

  1. Falana na son a saki Sowore

    Batun sake kama dan jaridar nan mai fafutuka a Najeriya, Omoyele Sowore na ci gaba da tayar da kura a kasar, har ma wasu na kira da a gudanar da bincike.

    Lauyan mutumin da aka sake kamawa, Femi Falana tuni ya sake nanata bukatar a saki mutumin da ya ke karewar tare da sauran duk mutanen da ake tsare su saboda siyasa a kasar.

    Ita dai fadar shugaban kasa ta nesanta shugaba Muhammadu Buhari daga batun sake kama Sowore.

    Sowore
  2. Alkaluman mamata na karuwa a Kenya

    Akalla mutum 10 ne suka mutu sakamakon rugujewar wani gini mai hawa shida a Tassia da ke wajen birnin Nairobi na Kenya ranar Juma'a.

    An ceto fiye da mutum 30 daga cikin buraguzan ginin kuma ana fargabar har yanzu akwai mutanen da ke cikin ginin da ba a kai ga cetowa ba.

    Ana fargabar alkaluman mutanen da suka mutu sakamakon ruguwar ginin ka iya ci gaba da karuwa.

    Kenya
  3. Ganduje da Sarki Sanusi

    Gwamnan jihar kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya nada Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, a matsayin shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta jihar.

    A wata sanarwa da babban sakataren hulda da 'yan jaridu na gwamnan, Abba Anwar, ya fitar a tsakar daren da ya gabata, ya ce, bias tanadin sashe na 4 (2) (g) da sashe 5 (1) (2) na dokar masarautun jihar ta 2019, gwamnan jihar ya nada, Alhaji Muhammadu Sanusi na II, Sarkin Kano a matsayin Shugaban Majalisar Sarakunan.

    Sanarwar ta kara da bayyana cewa daga cikin sauran 'yan majalisar akwai dukkanin sauran sarakunan jihar masu daraja ta daya, na Bichi da Rano da Karaye da Gaya, Alhaji Aminu Ado Bayero, Alhaji Dr Tafida Abubakar (Autan Bawo), Alhaji Dr Ibrahim Abubakar II da kuma Alhaji Ibrahim Abdulkadir.

    Ganduje da Sarki Sanusi

    Asalin hoton, BB