Abdelmajid Tabboune ne sabon shugaban Algeria

Wannan shafi zai rika kawo maku abin da ke faruwa kai-tsaye a Najeriya da Nijar da Ghana da kuma Kamaru, har ma da sauran kasashen Afirka masu makwabtaka.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Fauziyya Kabir Tukur

  1. Hisbah ta saki 'yan daudu 26 bayan yin sallar dare

    A ranar Lahadi ne hukumar Hisba ta Kano ta kama 'yan daudu guda 26 a lokacin wani casu a birnin.

    To sai dai a ranar Talatar ne kuma hukumar ta saki mutanen bayan sanya su yin sallar dare raka'a 40.

    An kama 'yan daudun ne sanye da kayan mata a cewar mataimakin kwamandan hukumar, Tasiu Ishaq.

    Daya daga cikin wadanda ake zargin ya ce an kama shi ne a wurin bikin wani abokinsa ne, amma wanda ya gayyace shin ya tsere a lokacin da 'yan Hisbah suka isa wurin.

    "Sun yi mana wa'azi kuma tun daga lokacin da suka tsare mu muna yin Sallah. Na yi nadamar abin da ya faru, kuma idan Allah ya yarda ba zan maimaita ba," inji shi.

    Abdullahi Ganduje ne gwamnan Kano
  2. Buhari ya nada sabon shugaban AMCON

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ba da sunan Edward Adamu a matsayin sabon shugaban kamfanin kula da kadarorin gwamnati.

    Sanarwar hakan na kunshe ne a cikin takardar da shugaban ya aike wa majalisar dattawan kasar a yau Talata.

    Hakan na zuwa ne yayin da wa'adin Muiz Banire ke karewa a matsayin shugaban kamfanin na AMCON.

    Buhari
  3. 'An yi kuskuren ba da kyautar Nobel', Abiy Ahmed bai cancanci kyautar Nobel ba

    'Yan kasar Eritrea a Scandinavia na gudanar da zanga-zangar adawa kan kyautar Nobel ta zaman lafiya da ake shirin bayarwa ga firai minista Abiy Ahmad.

    Da misalin karfe daya a agogon kasar Norway ne za a yi bikin bai wa Abiy kyautar.

    Kwamitin Nobel ne ya zabi firaminista Abiy Ahmed a matsayin wanda ya ci kyautar ta bana, saboda kawo karshen rikici da tsattsamar dangantaka tsakanin kasarsa da makwabciyarta Ethiopia da aka shafe fiye da shekaru ashirin ana yi.

    Masu zanga-zangar a Oslo sun ce alfanun sasanci tsakanin Eritrea da Ethiopia ba su tabbata ba, don haka Firai Minista Abiy bai cancanci kyautar ta Nobel ba.

    Daruruwan mutane ne ke zanga-zangar a birnin Oslo dauke da kwalaye dake cewa: "Kyautar Nobel ta tabbatacciyar zaman lafiya ce, ba siyasa ba."

    'Yan Eritrea a Norway na cewa firai minista Abiy Ahmed bai cancanci kyautar samar da zaman lafiya ta duniya ba.

    Asalin hoton, TT

    Bayanan hoto, 'Yan Eritrea a Norway na cewa firai minista Abiy Ahmed bai cancanci kyautar samar da zaman lafiya ta duniya ba.
  4. Malaman makaranta a Kenya za su bayyana kadarorinsu

    Gwamnatin Kenya ta bai wa malaman makarantan kasar mako biyu su bayyana kadarorinsu, kuma idan ba su yi hakan ba za a ci su tarar kudin kasar miliyan guda kwatankwacin dala dubu tara.

    Wannan dai na kunshe a cikin wata sanarwa da gwamnatin kasar ta fitar ranar Litinin.

    Shugaba Uhuru Kenyata na son ganin duk wani ma'aikacin gwamnati ya bayyana kadararsa a wani mataki na dakile matsalar cin hanci da rashawa.

    Malaman makaranta a Kenya za su bayyana kadara
  5. 'Hanyoyin da za a magance rashawa a Najeriya'

    Shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya zayya wasu matakai da ya ce idan aka bi su za a magance matsala rashawa da cin hanci a Najeriya.

    ·Dole ne jama’a su hada kai da hukumomi matsawar ana son magance matsalar

    ·A cire sanayya, duk wanda ya aikata cin hanci a hukunta shi, kamar yadda ake gani a kasashen da suka cigaba

    ·A daina alakanta abun da siyasa

    ·Masu fada aji su daina sanya baki a aiyukan hukumomin yaki da cin hanci da rashawa

    Shugaba Buhari ya sha alwashin yakar rashawa da cin hanci
  6. Fursunoni 5,000 sun samu afuwa a Tanzania

    Fursunoni 5,000 sun samu afuwa a wani mataki na rage cinkoso a gidajen yarin Tanzania.

    Shugaba John Magafuli ya sanar da afuwar ga fursunoni dubu biyar da dari biyar da talatin da uku, a lokacin bikin cikar kasar shekara 58 da samun 'yanci.

    Adadin shi ne mafi yawa da aka taba yi wa afuwa a Tanzania domin rage cinkoso a gidajen yarin kasar.

    Magafuli ya ce akwai fursunoni 35,803 a kasar, kuma fiye da rabinsu na zaman jiran a yanke musu hukunci ne.

    Shugaba Magafuli na Tanzania a lokacin bikin cikar kasar shekara 58 da samun 'yanci.

    Asalin hoton, AFP

  7. Bikin 'yancin dan adam a Nijer

    Jamhuriyar Nijar kamar sauran kasashen duniya na bikin zagayowar bikin cikar sanarwar bai daya ta kare hakkin bil'adama shekaru 71.

    Hukumar kula da kare hakin bil'adama ta kasar CNDH ce tare da kungiyoyin farar hula da ke fafutukar kare hakin dan Adam suka fitar da wata sanarwa ta hadin gwiwa suna kira ga hukumomin kasa da su samar da wata doka da za ta kare masu kare hakin dan Adam ganin yadda suke fuskantar baraza daga hukumomi.

    Shugaban Niger, Mahamadou Issoufou
  8. Gwamnatin Legas na kamen babura

    Rahotannin na cewa gwamnatin jihar Legas a Najeriya na kamen baburar achaba, bayan da gwamnatin ta kafa wani kwamitin aiki da cikawa.

    Bayanai na cewa 'yan kwamitin sun rinka bi gida-gida domin kwace baburan mutanen da suka fahimci suna achaba.

    Dama dai rundunar 'yan sandan jihar ta Legas kwace baburan fiye da guda 600 a baya-bayan nan.

    Akwai 'yan achaba da dama a birnoin Legas
  9. An kulle makarantu a Kamaru

    Gwamnatin Kamaru ta rufe makarantun kasar fiye da 260 wadanda ake gudanar da su ba bisa ka'ida ba.

    Ana dai gudanar da makarantun ne da manufar taimaka wa yaran da ke gudun hijra daga rikicin masu son ballewa daga kasar, a yankunan renon Ingilishi.

    Kamaru
  10. Yunwa na karuwa a Najeriya da Niger

    Wani rahoton kungiya mai fafutukar ganin kowa ya ci abinci mai suna Food Crisis Prevention Network, ya ce mutum milyan tara a Afirka ta yamma da kasashen Sahel na bukatar agaji sakamakon yawan tashe-tashen hankali da ke faruwa a yankunan.

    Rahoton ya bayyana cewa mutum milyan hudu daga yankin arewa maso gabas na Najeriya ne a gaba wajen neman taimakon abinci.

    Sai kuma jamhuriyar Nijer da Burkina Faso da ke da biye wa Najeriyar inda mutum milyan biyu ke bukatar agajin na abinci.

    .

    Yawaitar rikici ke sa yunwa karuwa a Najeriya da Niger
  11. An kashe sojoji biyu a Niger

    A Jamhuriyar Nijer, an kashe sojoji biyu yayin wani hari da aka kai kan sansanin sojin da ke kusa da garin Tillia na yankin Tahoua da ke iyaka da kasar Mali.

    Shafin intanet na ActuNiger ya rawaito cewa maharan sun tayar da bam ne a cikin wata mota domin samun damar kutsa wa ginin sansanin soji na Agando da ke garin na Tillia.

    Baya ga kisan sojojin guda biyu, maharan sun raunata wasu sojojin guda biyar.

    Kawo yanzu dai ba a tantance ko wace kungiya ce ta kai harin ba.

    Niger na fama da Boko Haram da 'yan tawaye
  12. Zaki ya tsinke a Nairobi

    Wani zaki ya tsinke daga wurin shakatawa na kasar Kenya da ke kudu da birnin Nairobi.

    Zakin wanda ya tsinke a jiya ya tumurmusa wani mutum a kan hanyarsa ta shiga gari.

    Hukumomi sun ce suna ci gaba da baza komar neman wannan dabba da ta tsinke domin mayar da ita mazaunninta.

    Babu dai wani bayani kan ko zakin ya yi kisa, sai dai al'ummar yankin da ake kyautata zaton zakin yana shawagi a ciki, na cikin fargaba.

    Zakin yana ta watangaririya
  13. Tsugune ba ta kare ba a Kano

    Masu nada Sarki a Kano sun maka gwamnatin jihar da majalisa a kotu, suna neman kotun ta taka wa gwamnatin jihar burki daga daukar duk wani mataki a kan sabuwar dokar masarautu ta jihar da gwamna Ganduje ya rattaba wa hannu a makon jiya.

    Masu shigar da karar dai sun hada Madakin Kano da Makama da Sarkin bai da sarkin dawaki mai tuta.

    Hakan dai na zuwa ne kwana biyu bayan gwamnan ya sanar da nada Sarki Sanusi a matsayin shugaban majalisar sarakunan jihar.

    Wadanda ake karar sun hada da kwamishinan shari'a na jihar da sabbin sarakunan da aka nada guda hudu.

    Sanusi
    Masu nada sarki guda hudu ne a Kano
  14. Masu bibiyarmu da fatan kun wayi gari lafiya. Ku ci gaba da kasancewa da shafin BBC Hausa domin kawo muku labarai da dumi-duminsu a yau Talata.

    Hausa
  15. Sojoji sun kashe 'yan Boko Haram 37

    A wani samame da sojojin Najeriya suka gudanar da manufar ci gaba da fatattakar 'yan kungiyar Boko Haram, sojojin sun ce sun yi galabar kashe 'yan kungiyar 37 sannan sun kwato motoci masu dauke da bindigogi guda hudu.

    Wata sanarwa da jaridar PR Nigeria ta aike wa da BBC, jagoran samamen, manjo janar Abdulmalik Bulama Biu, ta ce dakarun sun far wa 'yan Boko Haram inda suka lalata wurin da suke boye a Duguri Arge da ke kusa da Tumbus da Karere da Gashigar da Arege da Metele da kuma Malam fatori masu iyaka da tafkin Chadi.

    Jaridar ta PR Nigeria ta kara da cewa sojojin sun lalata motocin 'yan Boko Haram din masu dauke da bundugu da nakiyoyi da dai sauran makaman yaki.PR Nigeria ta kuma ce ta ga hotunan 'yan kungiyar da sojoji suka kashe tare da konawa.

    Sojoji sun kashe Boko Haram 37
  16. 'ISWAP ta kashe sojojin Najeriya biyu'

    Wani sabon bidiyo da yake yawo a intanet mai dauke da kwanan watan 8 Disamba ya bayyana yadda kungiyar IS a yammacin Afirka, ISWAP ta kashe wasu sojojin Najeriya guda biyu tare da wani dan sanda.

    Bidiyon wanda gidan talbijin na Channels TV ya samu ranar Litinin, ya bayyana yadda wasu 'yan bindiga wadanda fuskokinsu ke rufe da kuma ake kyautata zaton 'yan kungiyar ta ISWAP ne.

    Ana zaton an yi garkuwa da jami'an tsaron da aka kashe a bidiyon ne a wani shingen da 'yan kungiyar suka kafa garin Benisheikh, mai nisan kilomita 70 daga birnin Maiduguri na jihar Borno.

    ISWAP
  17. Girman rashawa da cin hanci a Najeriya

    Wani mai fafutukar yaki da rashawa a Najeriya, Malam Kabiru Dakata ya shaida wa BBC cewa, "lalacewar fannin shari'a ne babbar alamar da ke nuna irin girman rashawa da cin hanci a Najeriya."

    Dakata wanda jagoran kungiyar CAJA ne a jihar Kano, ya nuna takaici kan yadda aka hukunta sanata Orji Kalu bayan shekaru 12.

    Ya ce ya kamata tun tuni a ce an yanke wa tsohon gwamna hukunci, inda ya ce "irin wannan jan kafa ne ke kara sanya fargaba a zuciyar 'yan Najeriya dangane da aniyar gwamnati na yaki da rashawa da cin hanci."

    Kalu
  18. 'Yan Najeriya ba su damu da Sowore ba'

    Fadar shugaban Najeriya ta ce miliyoyin 'yan Najeriya ba bu ruwansu da sake kama dan jaridar nan, Omoyele Sowore a ranar Juma'a.

    Mai magana da yawun fadar shugaban na Najeriya, Femi Adesina wanda ya shaida wa gidan talbijin na Channels TV a shirin Sunrise Daily da safiyar Litinin.

    Sowore
  19. An fara gangami kan riga-kafin Ebola

    Rwanda da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo sun kaddamar da wani gangami kan riga kafin cutar Ebola ga mutanen da ke zaune a iyakar kasashen biyu.

    An kaddamar da kamfe din wanda aka yi wa lakabi da 'Umurinzi' wato mai karewa, a Grande Barriere, wata iyaka a yankin Rubavu kuma zai maida hankali ne kan mutanen da ke yawan tafiya tsakanin kasashen biyu kullum.

    Rwanda za ta yi wa mutane 200,000 daga yankunan Rubavu da Rusizi masu iyaka da DR Congo riga kafin, yayin da ita Jamhuriyar Demokradiyyar Congo za ta yi wa mutane 500,000 riga kafin musamman a yankunan da annobar Ebola ta shafa a gabashin kasar tun watan Agustan 2018.

    António Guterre
    Bayanan hoto, Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres a wata cibiyar bayar da magani a watan Satumba
    Ebola
  20. Orji Kalu zai ci gaba da karbar albashi

    Sanata Orji Kalu wanda yanzu haka ya ke gidan yari zai ci gaba da karbar albashi da sauran hakkokinsa kamar kowane sanata.

    Mai magana da yawun majalisar dattawan kasar, Sanata Godiya Akwashiki ne ya shaida wa jaridar PREMIUM TIMES ranar Lahadi.

    Sanata Akwashiki ya kara da cewa duk da an samu mista Orji Kalu da laifi kuma an yanke masa hukuncin zaman gidan kaso, har yanzu sanata ne kuma zai ci gaba da karbar albashi da sauran hakkokinsa.

    Ya kara da cewa idan dai har ba kotun koli ce ta yanke hukuncin karshe ba kan dan majalisar dattawan ba to Orji zai ci gaba da kasancewa sanata.

    Sai dai kuma mai magana da yawun majalisar ya ce kasancewar Orji Kalu sanata ba ya nufin zai rinka halartar zaman zauren majalisar ba.

    Kalu