Abdelmajid Tabboune ne sabon shugaban Algeria

Wannan shafi zai rika kawo maku abin da ke faruwa kai-tsaye a Najeriya da Nijar da Ghana da kuma Kamaru, har ma da sauran kasashen Afirka masu makwabtaka.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Fauziyya Kabir Tukur

  1. 'Karya ne Boko Haram ba su kashe sojojinmu ba'

    Rundunar sojin Najeriya ta ce bidiyon da ya rinka yawo a kafafen sada zumunta cewa 'yan Boko Hram sun kashe sojojinmu karya ne.

    Mai magana da yawun rundunar, Kanar Sagiru Musa, a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsu na Facebook, ya ce "batun cewa an kashe gomman sojojinsu ranar 10 ga watan Disamba zuki ta-malle ce."

    Sagir Musa ya alakanta bidiyon na boge da irin ayyukan kungiyar Biafra ta IPOB, inda ya ce suna yi ne da nufin tunzura al'umma.

    Ya kuma kara da cewa wani abu da ke nuna cewa kungiyar IPOB din ce ta kitsa bidiyon shi ne yadda wani mai suna Simon Ekpa wanda na daya daga cikin wadanda suka fito a cikin bidiyon yake kira ga masu bautar kasa 'yan kudu maso gabas da su bar yankin arewa maso gabas da kuma yin kira ga 'yan kabilar Igbo da su shiga aikin soji.

    Buratai

    Asalin hoton, AFP

  2. Za a fara bai wa 'yan Afirka bizar nan-take a Najeriya

    Gwamnatin Najeriya ta sanar da sauye-sauye a tsarin neman takardar biza ga 'yan sauran kasashen Afirka.

    Daga watan Janairun 2020, duka masu fasfo na wata kasa a Afirka za su iya neman takardar shiga Najeriya idan suka iso kasar, sabanin yadda aka saba a baya.

    A baya sai dai 'yan sauran kasashen Afirka su nemi takardar shiga Najeriya daga kasashensu na asali kafin su shiga Najeriyar.

    Shugaba Buhari ya ce jama'ar sauran kasashen za su iya hawa jirgi su je Najeriya ko ba su da takardar shiga, amma da zarar sun isa kasar za a ba su takaradar.

    Shugaban ya ce a shirye yake ya tallafa wa tsarin shiga kasashen juna ba tare da wani shamaki ba a Afirka.

    Buhari

    Asalin hoton, Getty Images

  3. Majalisa na jan kunnen kamfanin Berger kan titin Kano

    Majalisar wakilan Najeriya ta umurci Kamfanin Julius Berger da ke aikin sake gina hanyar Abuja zuwa Kano da ya bude sassan hanyar da ya kammala aikinsu.

    Kwamitin majalisar da ke kula da ayyuka ne ya ba da umurnin , lokacin da ya gana da shugabannin kamfanin.

    An dai gayyaci kamfanin sakamakon zargin da ake yi cewa aikin yana tafiyar hawainiya, ga kuma hadarin da ake yawan samu a kan hanyar, lamarin da ke haddasa asarar rayukan jama`a.

    Hon Abubakar Kabir Abubakar Bichi shi ne shugaban kwamitin, kuma ya shaida wa BBC cewa sun shaida wa kamfanin dole ne su kammala aikin a watanni 13 masu zuwa.

    Tunda fari dai kamfanin ya sha alwashin kammala aikin a cikin watannin 36, to amma yanzu an yi watanni 18 ba tare da cimma nasarar azo a gani ba.

    NASS

    Asalin hoton, NASS

  4. 'Mun janye yajin aiki'

    Kungiyar ma'aikatan kamfanin bayar da wutar lantarki ta Najeriya, ta sanar da janye yajin aiki.

    Kamfanin wutar na Eko da ke Legas ne ya bayar da sanarwar a shafinsa na Twitter ranar Alhamis.

    A ranar Laraba ne dai ta shiga yajin aikin al'amarin da ya jefa wasu bangarorin Najeriya cikin duhu.

    Kungiyar yana yajin aikin en dai saboda abin da ta kira rashin biyan tsoffin ma'aikatanta hakkokinsu da ya kamata.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Najeriya na fama da matsala rwutar lantarki

    Asalin hoton, Getty Images

  5. 'Za mu daga likkafar Dambe'

    Za mu bude shirin da Damben gargajiya, inda ministan wasannin Najeriya, Sunday Dare ya ce za su daga likkafar wasan ta hanyar sanya shi a jerin wasannin kasar.

    Dambe
  6. Ban kwana

    Nan muka kawo karshen rahotannin kai-tsaye.

    Ku duba kasa domin karanta abubuwan da suka faru a Najeriya da makwabtanta a yau Laraba ya zuwa yanzu da muke rufewa.

    Mu hadu gobe.

  7. Kofin Duniya: Afirka ta Kudu ta janye

    Afirka ta Kudu ta janye daga cikin jerin kasashen masu neman karbar bakuncin gasar cin kofin duniya na mata a 2023.

    Kungiyar kwallon kafar kasar ta ce ba za ta gabatar da takardu da bayanan neman karbar bakuncin wasan ba, da za a rufe a ranar Juma'a.

    Hukumar ta ce za ta mayar da hankali ne a kan inganta wasannin mata musamman gasar kasar kafin ta sake neman karbar bakuncin gasannin duniya.

    Mastalar tattalin arziki na daga cikin abubuwan da suka kawo cikas ga shirin kasar na neman karbar bakuncin gasar.

    Kungiyar kwallon kafa ta Afirka ta Kudu

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Kungiyar kwallon kafa ta Afirka ta Kudu
  8. Tsawon rai ya karu a Ghana, Karuwar shekara 7 ya ba wa Ghana maki 155

    Hukumar kula da cigaban kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya (UNDP) ta ce tsawon ran 'yan kasar Ghana ya karu da shekara 7.

    Rahoton da hukumar ta fitar ya ambato rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya na 2018 da ke nuna cewa tsawon kwanan maza a Ghana ya kai shekara 62.2, mata kuma shekara 64.4.

    Rahoton ya ce gaba daya, tsawon ran mutanen Ghana ya kai shekara 63.4.

    Hakan ya sa tsawon rai a kasar ke a matsayi na 155 a fadin duniya.

    Kofar Black Star Gate da ke birnin Accra

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Kofar Black Star Gate da ke birnin Accra
  9. Masarautun Kano: Martanin gwamnati ga umurnin kotu, Kotun ta hana gwamnatin jihar kafa majalisar sarakuna

    Aminu Ado Bayero shi ne Sarkin Bichi

    Asalin hoton, Salihu Tanko Yakasai

    Bayanan hoto, Gwama Ganduje da Aminu Ado Bayero, daya daga cikin sabbin sarakunan da ya nada

    Gwamnatin jihar Kano ta mayar da martani ga umurnin babbar kotun jihar da ta dakatar da gwamnatin daga kafa sabbin masarautu a jihar.

    Kwamishinan yada labaran jihar Garba Muhammad ya fitar, ya ce umurnin kotun bai shafi samuwar sabbin masarautun da gwamnatin jihar ta kafa ba.

    Sai dai kuma Antoni Janar kuma kwamishinan shari'ar jihar ya ba wa BBC tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta bi umurnin kotun game da matsayin masu nada sarki.

    Kotun ta bayar da umurnin ne kwana biyu bayan gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya nada sarkin Kano Muhammadu Sanusi a matsayin shugaban majalisar sarakunan.

    Masu nada sarki a Masarautar Kano ne suka shigar da karar suna neman kotun ta dakatar da gwamnatin da majalisar dokokin jihar kafa sabbin masarautun Bichi da Gaya da Karaye da kuma Rano da kuma kafa majalisar sarakunan jihar.

    Kotu za ta cigaba da sauraron karar a ranar 17 ga watan Disamban nan da muke ciki.

  10. Kwastam sun harbi dalibi a Kano

    Rahotanni na cewa jami'an hukumar kwastam a Najeirya sun harbi wani matashi dalibi a birnin Kano wanda dan asalin jihar Yobe ne.

    Dalibin ya ce jami'an dai sun bude wuta a kan motarsa ne bayan ya taka burkin gaggawa sakamakon ankarar da ya yi da shingen da jami'an suka kafa a kan hanyarsa ta shiga birnin Kano daga jihar Yobe.

    Ya ce sun yi zargin mai fasakauri ne, amma bayan da suka lura cewa ba haka ba ne sai suka ranta a na kare.

    Hamid Ali

    Asalin hoton, Customs site

  11. Al-Bashir ya gurfana a gaban kotu

    Omar al-Bahir na iya fuskantar hukuncin kisa ko daurin rai ai iya idan yaka same shi da laifin juyin mulki

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, An dauki hoton Omar al-Bashir a gidan yarin Kober a watan Yuni

    Hambararren shugaban Sudan Omar al-Bashir ya gurfana a gaban kotu bisa zargin juyin mulkin da ta kawo gwamnatinsa a 1989 a kasar.

    A watan Nuwamba ne aka kafa wani kwamintin bincike a kasar bayan hukumomin kasar sun tuhumi al-Bashir da wasu hadimansa da shirya juyin mulki.

    Idan aka same shi da laifi tsohon shugaban wanda ke tsare a gidan yarin Kober na iya fuskanatar hukuncin kisa ko daurin rai da rai.

    Ana kuma tuhuma al-Bahir din da laifin tunzurawa da kuma hannu a kisan masu zanga-zanga.

    Bayan haka ana ana sa ran kotu za ta yanke masa hukucin a wani karar da aka shigar na zarginsa da zamba da kuma mallakar kudaden kasashen waje ba bisa ka'ida ba.

  12. Mutum 10 sun mutu a harin Somalia

    'Yan sanda a Somaliya sun ce sun kawo karshen harin da maharan al-shabab suka kai wani otal da ke Mogadishu baban birnin kasar.

    An kashe jami'an tsaro guda biyu da fararen hula guda uku sannan an kashe maharan guda biyar a lokacin artabun.

    Wata sanarwar da 'yan sanda suka fitar ta ce an ceto akalla mutum 82.

    Maharan da sojoji sun fara artabun ne a wajen wani shingen da ke kai wa ga gidan shugaban kasa.

    al shabab ce kungiyar mayaka a Somalia

    Asalin hoton, Getty Images

  13. An cire haraji a kan audugar mata.

    An soke karbar haraji a kan adugar mata, domin saukaka farashinsu a kasar Rwanda.

    Ministar jinsi da iyalai ta kasar sanar da haka.

    A baya ana karbar harajin kashi 18 a kan audugar wadda ake sayar da fakitinsa a kan Franc 1,000 (kimanin dala 1.07).

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Sai dai masu fafutuka a kasar na korafin cewa tsadar farashin ya sa musmman 'yan mata da masu karamin karfi da mazauna karkara ba sa iya sayen audugar.

    Hakan ya sa har yanzu wasunsu ke cigaba da amfani da kunzugu, abin da ke kara jefa su cikin hadarin kamuwa da cututtuka, a cewar Saidath Murorunkwere mai fafutakar kare hakkin mata.

    Aline Berabose, mai fufutukar kare lafiyar mata na cewa 'yan mata da suka fito daga gidaje masu karamin karfi kan yi fashin makaranta a lokacin al'adarsu saboda ba su da halin samun audugar.

    Tsadar farashi ta sa audugar al'ada ta fi karfin wasu mata Rwanda

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Wasu matan ba sa iya sayen audugar al'ada saboda tsadarsa a Rwanda
  14. Kotu ta kori karar da Nnamdi Kanu ya shigar

    Kotun ECOWAS ta kori karar da jagoran masu fafutukar ballewa daga Najeriya, IPOB, Nnamdi Kanu wadda ya shigar gaban kotun bisa zargin gwamnatin Najeriya da take masa hakkinsa na dan adam.

    Nnamdi Kanu dai ya shigar da karar ne cewa jami'an tsaron Najeriya sun azabtar da shi da cin zarafinsa da kuma kwace masa wasu kadarorinsa.

    Nnamdi Kanu

    Asalin hoton, Getty Images

  15. Mutum 17 sun mutu a harin da 'yan bindiga suka kai wa sojojin Nijar, Sun kai wa sojojin hari

    Sojoji a Jamhuriyar Nijar sun hallaka 'yan bindiga da suka kai wa wani sansanin soji hari a yankin Tahoua da Inates.

    Ministan tsaron kasar ya ce sojojin sun yi ta musayar wuta na tsawon sa'a biyu bayan 'yan ta'addan da ke cikin gwamman motoci sun bude masu wuta.

    Ministan ya ce dauki ba dadin ya yi sanadiyyar mutuwar jami'an soji guda uku da kuma hallaka 'yan ta'adda guda 14.

    Ya ce sauran 'yan ta'addan tserewa zuwa yankunan kasar Mali.

    Kasar na daga cikin kasashen yankin Sahel da ke fama da barazaran kungiyoyi masu dauke da makamai irin su IS da Al-qaeda.

    Jamhuriyar Nijar
  16. Aisha Buhari ta caccaki Garba Shehu

    Mai dakin shugaba Muhammadu Buhari, Aisha Buhari ta wallafa wani rubutu da yake ta karakaina a shafukan sada zumunta, inda da kanta ta caccaki mai magana da yawun Buhari, malam Garba Shehu.

    Rubutun da aka wallafa mai taken "Garba Shehu na wuce gona da iri", mai dakin shugaba Buharin ta nuna yadda mai magana da yawun mijin nata ke 'yi wa iyalan shugaban zagon kasa'.

    Aisha Buhari ta ce "Garba Shehu na daya daga cikin masu kware wa Buhari baya kasancewar yaron abokin hamayyar Buharin ne a zaben shugaban kasa, Alhaji Abubakar."

    Ta kuma yi zargin Garba Shehu da yin sama da fadi da wasu kudaden 'yan jaridu a fadar shugaban kasa.

    Har wa yau, Aisha Buhari ta nuna rashin jin dadinta dangane da yadda Garba Shehu yaki cewa uffan a lokacin da ake yada jita-jitan auren Buhari da minista Sadiya Farouk.

    To sai dai da BBC ta tuntubi Malam Garba Shehu kan batun, ya ce ba zai sa-in-sa da mai dakin mutumin da yake yi wa aiki ba.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Aisha Buhari
  17. Najeriya da Kamaru na cikin kasashen da aka fi daure 'yan jarida, Abin ya fi tsanani a Masar da Eritrea da Kamaru, inji rahoton

    Kwamitin kare 'yan jarida ya ce kasashen Masar da Eritea da Kamaru ne aka fi tsare 'yan jarida a gidan yari fadin duniya.

    Kasar Eritrea ita ce kasasr da ta fi kame 'yan jarida daga cikin kasashen yankin Sahara 16 da ke kame 'yan jarida.

    A sakon da ta wallafa a shafinta na tuwita, jami'ar kwamitin mai kula da yankin Sahara Angela Quintal ta bayyana jerin kasashen da 'yan jarida suka fi fuskantar barazana yayin gudanar da aikinsu a yankin.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Rahoton ya tattara sunayen 'yan jarida 39 da aka daure a Masar, wadda ita ce matsalar ta fi kamari. Yawancin wadanda yawancinsu aka gurfanar da su a gaban kotu da zargin ayyukan ta'addanci da yada labarun karya.

    Yawancin 'yan jaridan da aka tsare a Masar a baya-bayan na an kama su ne gabanin zanga-zangar zargin rundunar sojin kasar da mundahana. Shugaban kasar Abdul Fattah al-Sisi tsohon jami'in rundunar ne kafin ya hau mulki, a cewar kwamitin.

    Kasar Eritrea ita ce kasasr da ta fi kame 'yan jarida daga cikin kasashen yankin Sahara 16 da ke kame 'yan jarida.

  18. 'Mun bar Punch da 'yan Najeriya domin alkalanci'

    Mai magana da yawun Shugaba Muhammadu Buhari, Malam Garba Shehu, ya ce kokarin jaridar Punch na kakaba wa Shugaba Buhari lakabin 'dan kama-karya' siyasa ce tsagwaronta.

    Ya ce jaridar ta buga misali da cewa gwamnatin Buhari na take hakkokin 'yan kasa da suka hada da Omoyele Sowore.

    Garba Shehu ya kara da cewa Sowore ya yi abin da ya yi ne da sunan siyasa ba jarida ba.

    Dangane kuma da makala wa Buhari lakabin mai kama-karya, Garba Shehu ya ce jaridar ta yi yunkurin yi wa tsarin mulkin Najeriya da ya bai wa Shugaba wannan dama, karan tsaye.

    To sai dai daga karshe mai magana da yawun Shugaba Buharin ya ce babu wani matakin doka da za su dauka kan jaridar illa dai su bar ta da 'yan kasa domin alkalanci.

    Ana zargin Buhari da take hakkin dan adam
  19. Ambaliya ta shafe gidaje 700, ..ta kuma mamaye wuraren hakar ma'adinai

    Ruwan sama kamar da bakin kwarya ya yi sanadiyyar ambaliyar da ta mamaye unguwanni da wuraren hakar ma'adinai.

    Akalla gidaje 700 ne ambaliyar ta yi awon gaba da su, baya ga daidaita jama'a a Pretoria, babban birnin kasar Afrika ta Kudu.

    Ambaliayar ta kuma mamaye tashar wutar lantarkin yankin, abin da ya kawo tsaiko ga ayyukan lantarki a tashar.

    Hakan ya tilsatsa dakatar da hakar zinare da lu'ulu'u.

    Kamfanin harkar lu'ulu'u na Petra Diamonds ya ce ya dakatar da ayyukansa a karkashin kasa domin kauce wa barnar abaliyar.

    Ambaliyar da ta biyo bayan ruwa kamar da bakin kwarya a Afirka ta Kudu

    Asalin hoton, EPA

  20. Kotun ECOWAS ta nemi gwamnatin Najeriya ta biya diyya

    Kotun ECOWAS ta umarci gwamnatin Najeriya da ta biya naira miliyan 52 a matsayin diyya ga iyalan matukin motar man nan da sojojin kasar suka harbe ranar 26 ga watan Disamban 2010.

    Yayin zamanta na jiya Litinin, kotun ta ware nair amilyan 50 ga 'ya'yan mutumin su takwas da suka shigar da karar, inda ta ware naira milyan biyu da rabi a matsayin kudin da aka kashe wajen shigar da karar.

    ECOWAS

    Asalin hoton, ECOWAS