Abdelmajid Tabboune ne sabon shugaban Algeria

Wannan shafi zai rika kawo maku abin da ke faruwa kai-tsaye a Najeriya da Nijar da Ghana da kuma Kamaru, har ma da sauran kasashen Afirka masu makwabtaka.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Fauziyya Kabir Tukur

  1. An kama buhu 700 na tabar wiwi a Edo, Curarren tabar wiwi guda 545 ne aka kama a wata maboya

    Hadin gwiwar hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi NDLEA da rundunar soji a Najeriya ta kama buhu 725 na tabar wiwi. Sun kuma yi nasarar kwato bindigogi takwas kirar gida daga hannun bata garin.

    Hukumomin sun kama buhunan curarren tabar wiwi guda 545 ne aka kama da daya daga cikin maboyar, baya ga wasu buhu 113 da aka kama a wani wuri, da kuma wasu 73

    An kama buhunan tabar wiwin da aka cuccure ne a wasu manyan buhuna, Mai magana da yawun runduna ta hudun sojin Najeriya a Benin, Manjo Ojo Adenegan, ya ce ma'ajiyar tabar winin na wasu maboya uku ne a cikin kungurmin jeji a karamar hukumar Owan ta Yamma a jihar Edo.

  2. Kamaru, Yankin rainon Ingila na iya samun karuwar 'yanci

    Paul Biya

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokokin Kamaru za ta fara muhawara kan wani kudirin doka da ka iya kara wa yankin kasar na rainon Ingila 'yanci.

    An bayyana kudirin dokar ne yau a wani taron hadin-gwiwa na majalisun dokokin kasar da za a kwashe tsawon kwanaki 15 ana yi.

    Taron na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da tattauna yadda za a gano hanyoyin magnace rikici a yankin rainon Ingila da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 3000 da kuma daidaita wasu mutanen 700,000.

  3. Coci ta hana sanya siket da wando jeans

    Wata coci a birnin Nairobi na kasar Kenya ta haramta sanya siket ko wando jeans idan za a shige ta bisa hujjara cewa hakan ya saba al'adar cocin.

    Cocin St Peter's Claver Catholic Church ta kafe wani hoto da ke nuna yanayin sa tufafi guda 10 da ba ta amince masu bauta a cocin su sanya ba.

    To sai dai cocin ba ta bayani ba dangane da hukuncin da za ta dauka idan aka karya dokokin da ta shimfida.

    Cocin ta gargadi masu bauta kan kayan da ya kamata su sanya

    Asalin hoton, Getty Images

  4. Abdelmajid Tabboune ne sabon shugaban Algeria

    Abdelmadjid Tebboune ya lashe zaben Algeria da kaso 58 na kuri'un da aka kada kamar yadda hukumar zaben kasar ta tabbatar.

    Hukumar ta kuma tabbatar da cewa an samu kaso 40 na fitowar masu zabe irinsa mafi karanci ga tsarin siyasar kasar.

    Mutane da dama dai ne suka kaurace wa zaben a wani mataki na nuna rashin amince wa da dukkanin 'yan takarar shugabancin kasar bisa zargin kusancinsu da tsohon shugaban kasar.

    Abdelmajid Tebboune, mai shekara 74, tsohon ma'aikacin gwamnati ne inda a 2017 ya zama firai minista na wata bakwai kacal sakamakon rikici tsakaninsa da 'yan kasuwar kasar masu fada aji.

    Tebboune ya kuma kasance tsohon ministan gidaje da yada labarai

    Sabon shugaban Algeria, Abdelmajid Tabboune

    Asalin hoton, Getty Images

  5. Najeriya na da kananan yara masu kanjamau

    Karamin ministan lafiyar Najeriya, Sanata Adeleke Mamora, ya ce Najeriya ce tafi kowacce kasa yawan jariran da ke dauke da kwayar cutar HIV mai karya garkuwar jiki.

    Ya ce hakan ne ya sa gwamnati za ta ci gaba da gudanar da al'amaurna da suka shafin samar da garkuwa daga kamuwa da wannan kwayar cutar a fadin kasa.

    Sanata Mamora kamar yadda jaridar Punch ta rawaito, ya ce gwamnati za ta zuba makudan kudade da ma'aikata da kayan aiki wajen ganin an dakile kamuwa da wannan cuta mai karya garkuwar jiki zuwa 2030.

    HIV

    Asalin hoton, Getty Images

  6. Ma'aikatan INEC za su kwashe shekara 12 a gidan kaso

    Wata babbar kotu a Najeiya ta daure wasu ma'aikatan hukumar zaben kasar hukuncin daurin shekara 21 kowannensu saboda samun su da laifin karbar cin hanci da rashawa.

    Kotun ta kuma ba da umarnin kamo wata tsohuwar minista a zamanin gwamnatin tsohon shugaba kasar Goodluck Jonathan, da ta ce jami'an sun karbi cin hancin daga wajenta.

    Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasar EFCC ce ta shigar da karar, tana tuhumar ma'aikatan na INEC a jihar Adamawa, da suka hadar da Ibrahim Mohammed Umar, da Sahabo Iya Hamman, da karba rashawar naira miliyan dari uku da sittin daga hannun tsohuwar ministar man fetur Diezani Alison Maduke, da nufin amfani da su wurin yin magudi a zaben shugaban kasar na 2015.

    Shugaban hukumar INEC ta kasa, Mahmud Yakubu

    Asalin hoton, Getty Images

  7. Heftar ya yi kira da a kutsa Tripoli domin kame ta

    Janar Khalifa Heftar mai karfin fada aji a sojin kasar Libya, ya yi kira ga dakarun kasar da su kutsa da manufar kame birnin Tripoli.

    Khalifa Heftar ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya gabatar na ba-sabun-ba a gidan talbijin na kasar.

    A watan Afrilu ne dai Heftar ya gudanar da wani babban yunkurin mamaye birnin wanda ke karkashin ikon dakarun gwamnati da Majalisar Dinkin Duniya ke mara wa baya.

    Rahotanni na rawaito cewa an samu karin tayar da kayar baya daga sojoji a yankin tun bayan wannan sanarwa.

    Khalifa Heftar ya nemi da a kutsa birnin Tripoli
  8. An dage shari'ar 'yan luwadi a Najeriya

    An dage shari'ar da ake yi wa wasu maza 47 da suke bayyana soyayya ga juna a bainar jama'a har zuwa watan Fabrairu.

    Karo na biyu dai kenan da mai shigar da kara na gwamnati ya gaza bayar da shaida kan zarge-zargen da suke yi wa wadanda ake tuhumar.

    An dai kama mutanen yayin wani bikin murnar zagayowar ranar haihuwa a 2018, kuma dukkannin su sun ki amsa laifin.

    A lokacin da aka kama mutanen sai da aka nuna su a gidan talbijin na kasa, al'amarin da wasu daga cikinsu suka shaida wa BBC cewa ya raba su da danginsu da ma ayyukansu.

    Wasu daga cikinsu sun yi asarar ayyukansu
  9. An gayyaci matar Omar al-Bashir amsa tambayoyi

    An gayyaci mai dakin tsohon shugaban Sudan, Omar al-Bashir, Widad Babiker zuwa ofishin mai shigar da kara na gwamnati domin amsa tambayoyi kan wasu kadarorinta da ma asusunta na bankuna.

    Widad Babiker wadda aka yi wa daurin talala tun bayan tunbuke mai gidanta a watan Afrilu an kai ta ofishin mai kara na gwamnati ranar Alhamis.

    Rahotanni na cewa akwai yiwuwar ba za a sake ta domin komawa gida da wuri ba.

    Widada Babiker

    Asalin hoton, AFP

  10. An yi jana'izar sojojin da aka kashe 73

    Shugaban kasar, Mohamadou Issoufou ne ya jagoranci jana'izar sojojin 71 da kungiyar IS ta hallaka yayin harin da ta kai kan wani sansanin sojin kasar a yankin Tillabery ranar Talata.

    Tuni dai shugaba Issoufou ya sanar da fasa gudanar da bukukuwan bikin cikar kasar shekara 59 da samun 'yancin kai da za a yi ranar Laraba mai zuwa a birnin Niamey.

    Da ma dai Mahamadou Issoufou ya snaar da katse ziyarar aikin da yake yi a Misra lokacin da ibtila'in ya faru, domin nuna alhinin rashin dakarun nasa.

    Mhamadou Issoufou

    Asalin hoton, BB

    Sojoji 73 ne suka mutu
  11. Farawa

    Masu bibiyarmu barkanku da warka da sake saduwa a ranar Juma'a wadda Hausawa ke yi wa kirari 'Juma'atu babbar rana'.

    Da fatan za ku kasance da mu domin kawo muku wainar da ake toyawa a Najeriya da Niger da Kamaru da Chadi da ma sauran kasashen Afirka.

  12. Saliyo, 'Haramta wa 'yan mata masu ciki zuwa makaranta ba dai-dai ba ne'

    Wata kotun ECOWAS ta yanke hukuncin cewa matakin da gwamnatin Saliyo ta dauka na haramta wa 'yan mata masu ciki zuwa makaranta ya kauce wa ka'ida kuma ya kamata a gaggauta soke shi.

    Matakin kotun ya samu goyon bayan kungiyoyin kare hakkin dan Adam irinsu Amnesty International.

    Kotun ta ce hukuncinta zai zama darasi ga sauran kasashe masu irin wannan haramcin kamar Tanzaniya da Equitorial Guinea.

    Kotun ta ce haramta wa 'yan matan zuwa makaranta nuna wariya ne kuma ya kauce wa dokokin kare hakkin bil Adama.

    Gwamnatin Saliyo ta kakaba haramcin ne shekaru hudu da suka gabata, lokacin da aka samu karuwar 'yan mata masu samun ciki a waje saboda illar da cutar Ebola ke yi.

    Gwamnatin ta ce dalilin haramcin shi ne saboda 'yan matan ba za su samu kuzarin zuwa makaranta ba kuma za su gurbata tarbiyyar kawayensu.

    An bude makarantun na musamman saboda 'yan mata masu ciki amma kungiyoyin kare hakkin dan Adam sun ce hakan bai isa ba.

    Pregnant Teen

    Asalin hoton, Getty Images

  13. Ya kamata tsarin mulki ya fadada bangaren Shari'ar Musulunci – Alkalin Alkalan Najeriya

    Alkalin alkalan Najeriya

    Asalin hoton, Others

    Wasu 'yan Najeriya sun fara tayar da jijiyoyin wuya game da kiran da Alkalin Alkalan Najeriya ya yi na gyara kundin tsarin mulkin Najeriya domin fadada bangaren shari'ar Musulunci.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito Mai Shari'a Muhammad Danjuma yana yin kiran a madadin Alkalin Alkalai Mai Shari'a Ibrahim Tanko Muhammad a wurin taron alkalai na shekara-shekara da aka gudanar a Jami'ar Ahmadu Bello, Zaria ranar Laraba.

    Ibrahim Tanko ya ce wannan yunkuri zai yiwu ne idan jami'oi a Najeriya suka ware wa Shari'a sashenta daban, ba kamar yadda yake a yanzu ba.

    Ya ce: "Kamar yadda muka sani akwai wani sashe na kundin tsarin mulki da ya bayar da damar aiwatar da tsarin Shari'ar Musulunci, amma bayan haka babu abin da za mu iya yi.

    "Muna da yawan da za mu iya kawo wannan sauyi, kuma idan muna so to sai mun sauya tsarin mulki domin ya dace da bukatummu na Musulmai."

    Tun da farar safiyar Alhamis ne shafin Twitter ya cika da ra'ayoyin wasu 'yan Najeriya, inda maudu'in #Shari'a yake ta tashe.

    Sai dai akasarin kalaman na batanci ne ko kuma sun yi tsaurin da ba za mu iya saka su a nan ba.

  14. DSS ta gayyaci mai buga jaridar intanet ofishinta

    Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya ta gayyaci wani mai wallafa jarida a intanet mai suna Newsdiary, Danlami Nmodu mni don amsa tambayoyi.

    Wasu jaridun Najeriya sun ruwaito cewa wani jami'in DSS da ya kira Danlami a waya ranar Laraba ya ce gayyatar ta jibanci wani labari da jaridar ta buga kwanan nan kan ayyukan Asusun Kare Muhalli na jihar Kano.

    DSS ta bukaci Danlami Nmodu ya je ofishin nata ranar Larabar ko kuma Alhamis da safe.

  15. An kai Faisal Maina gidan gyaran hali na Kuje

    Alkalin wata babbar kotu a Abuja, Mai shari'a Okon Abang ya bayar da umarnin mayar da Faisal Maina dan gidan tsohon shugaban kwamitin yi wa tsarin fanshon Najeriya garanbawul, Abdulrasheed Maina, zuwa gidan gyara hali na Kuje.

    A ranar Laraba ne dai alkalin ya bayar da wannan umarni bayan Faisal ya kwashe makonni a tsare a hannun 'yan sanda.

    A ranar 25 ga watan Oktoba ne dai aka gurfanar da Faisal a gaban kuliya bisa tuhuma guda uku da suka hada da safarar kudade da kuma mallakar asusun banki ba bisa ka'ida ba.

    Faisal Maina
  16. Kamaru, Shugaba Biya ya kira zaman hadin-gwiwar majalisun dokoki

    Gabanin cikar wa'adin Majalisa Dinkin Duniya na daukar mataki kan rikicin yankin rainon Ingilishi a mako mai zuwa, Shugaba Paul Biya ya kira taron majalisun kasar biyu ranar Juma'a.

    Babu wani karin bayani kan gayyatar, amma ana tunanin cewa yana da nasaba da matsayi na musamman da aka bai wa yankin da ma wasu yankunan kasar.

    Shugaba Paul Biya

    Asalin hoton, Getty Images

  17. Muna kira da a saki El-zakzaky - IMN

    Kungiyar 'yan Shi'a karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim Elzakzaky, IMN, ta yi kira ga gwamnatin Shugaba Buhari da ta saki jagoranta da ya kwashe shekaru hudu cif-cif yana hannun hukuma tun bayan rikicin da 'yan kungiyar suka yi da sojoji a Zaria a 2015.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar ta IMN, Ibrahim Musa ya fitar, kungiyar ta ce "Yayin da muke bikin zagayowar ranar kisan kiyashin Zaria da mutuwar mambobin IMN, muna kira da a gaggauta sakin Sheikh tare da duk sauran jama'ar da ke tsare ba tare da wani sharadi ba."

    IMN ta kuma bukaci da a hukunta dukknain sojojin da suke da hannu a 'kisan mutum kusan 1000' da kungiyar ta yi zargin an yi a Zaria.

    IMN

    Asalin hoton, Others

  18. An tarwatsa zaben shugaban kasar Algeria

    Masu zanga-zangar kin amincewa da zaben shugaban kasa a Algeria sun tarwatsa rumfunan zabe a yankin Kabylie da ke gabas da Algiers babban birnin kasar.

    Ana gudanar da zaben ne bayan tilasta wa tsohon shugaba Abdelaziz Bouteflika, yin murabus bayan shekara 20 yana jagorancin kasar.

    Bouteflika ya sauka ne a watan Afrilu bayan zanga-zangar kyamar gwamnatinsa da aka shafe makonni a na yi a kasar.

    Masu zanga-zangar sun cigaba da bukatar kakkabe ragowar jami'ai da mukarraban gwamnatin Abdelaziz Bouteflika, daga shugabancin kasar.

    Suna kuma barazanar kaurace wa zaben na yau Alhamis. Akalla rumfunan zaben guda biyu ne cincirindon masu zanga-zangar suka mamaye a yankin inda suka tarwatsa al'amura.

    Dukkan 'yan takara biyar a shugaban kasar na yau Alhamis mukarraban tsohon shugaban ne.

    Masu lura da al'amura na ganin rundunar sojin Algeria na tunanin cewa zaben ita ce kadai hanyar da za ta daidaita al'amura a kasar.

    Masu zanga-zangar na neman a kakkabe ragowar mukarraban gwamnatin Abdelaziz Bouteflika

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Dukkan 'yan takara biyar a zaben mukarraban tsohon shugaba Abdulazeez Bouteflika ne.
  19. Al-Shabab ta kai hari sansanin soji a Mogadishu

    Al-shabab attack

    Asalin hoton, Reuters

    Gwamman mayakan al-Shabab sun kai hari kan wani sansanin soji a Somaliya.

    Wasu da suka shaida lamarin sun ce mayakan sun mamaye sansanin Hilweyn a Mogadishu babban birnin kasar kuma sun lalata motoci da gine-gine kafin suka janye.

    Majiyoyin rundunar sojin kasar sun ce dakarun gwamnati sun janye kuma na kashe masu soja daya.

    Wanda suka shaida lamarin sun ce fararen hula hudu sun mutu a harin na daren Alhamis.

    Al-Shabab ta ce ta kashe sojoji 4.

  20. Ghana, Ana fuskantar hauhawar farashi a Ghana

    Hauhawar farashi a Ghana ta karu sosai a watanni hudu bayan da babban bankin kasar ya kaddamar da sabon ma'unin gwada hauhawar farashi a watan Agusta.

    Duk da da cewa an yi hasashen daidaita hauhawar farashin, kudin cedi ya fadi kuma wannan ya taimaka wajen kara farashin kayayyaki a Ghana.

    Kudin Ghana na Cedi

    Asalin hoton, Getty Images