Wata kotu a jihar Zamfara da ke arewacin Nijeriya ta bayar da umarnin tsare wani tsohon kwamishina a jihar Ibrahim Dan Malikin Gidan Goga a gidan yari har zuwa 12 ga watan Disamba.
A ranar Talatar ne kotun ta ba da umarnin kai tsohon kwamishinan gidan yari, bayan an gurfanar da shi gabanta bisa tuhumar bata sunan gwamnan jihar ta Zamfara Bello Matawallen Muradun.
'Yan sanda sun kama tsohon kwamishinan nan ne a ranar Litinin, bisa zargin tunzura jama’a, kamar yadda sammacin kama shi ya nuna.
Makusantansa sun shaida wa BBC cewa an tsare shi a sashin binciken manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan jihar.
Sun yi zargin cewa an kama shi ne bisa umarnin gwamnan jihar Bello Matawalle, sai dai mai magana da yawun gwamnan, Yusuf Idris ya musanta cewa akwai hannun gwamnati a kamen.
Ya shaida wa BBC cewa ‘yan sanda ne kawai suka kama Ibrahim Dan Malikin, ba tare da saka hannun gwamnatin jihar ba.
A ranar Asabar din da ta gabata ne dai Ibrahim Dan Maliki ya mayar wa gwamna Matawalle martani kan zargin da ya yi cewa tsohon gwamnan jihar Abdulaziz Yari ne yake haifara da tashe-tashen hankula da kashe-kashe a jihar.
A hirarsa da BBC, Gwamna Matawalle ya yi barazanar kama Abdulaziz Yari idan ya sake shiga jihar aka samu tashin hankali.
Bangaren tsohon gwamnan dai sun musanta wadannan zarge- zarge.