Kano Pillars ta sayi ƙarin 'yanwasa biyu

Asalin hoton, Kano Pillars
Ƙungiyar ƙwallon ƙfa ta Kano Pillars ta ɗauki ƙarin 'yanwasa biyu domin ƙarfafa tawagar ta mai horarwa Ogenyi Evans kafin fara kakar wasa ta 2025-26.
A ranar Laraba ta sanar da sayen ɗanwasan tsakiya Olakunle Alaka daga ƙungiyar Akwa United kan yarjejeniyar shekara biyu.
A ranar dai ta sake sanar da ɗaukar ɗanwasan gaba Aliyu Umar daga Niger Tornadoes kan kwantaragin shekara biyu shi ma.
Sanarwar na zuwa ne bayan nasarar lashe kofin Gusau/Ahlan da aka fafata a jihar Nasarawa ranar Juma'ar da ta gabata, inda ta doke Plateau United a bugun finareti.
A ranar Lahadi kuma Pillars za ta fara buga gasar NPFL ta bana a gidan Abia Warriors da ke garin Umuahia na jihar Abiya.



















