Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 15/06/2025

Rahoto kai-tsaye

Ahmad Bawage

  1. Mahara sun hallaka mutum 45 a jihar Benue

    Benue

    Asalin hoton, AFP vis Getty Images

    Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia ya yi Alla-wadai da da hare-hare da aka kai jihar, waɗanda suka janyo mutuwar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

    Gwamnan ya ce babu abin da zai sa a salwantar da ran ɗan'adam.

    Ya kuma ce ba zai gajiya ba har sai ya samar da zaman lafiya a jihar.

    Jami'ai sun ce aƙalla mutum 45 ne aka kashe yayin wani hari da aka kai cikin dare a jihar Benue.

    Shaidu sun ce ana zargin wasu makiyaya da kai harin, inda ƴansanda suka ce sun yi artabu da maharan.

    An ƙona gidaje da dama a harin da aka kai garin Yelewata.

    Rikici tsakanin manoma da makiyaya dai ba sabon abu bane a Najeriya.

    Mutum 25 ne suka mutu kwanaki biyu da suka gabata bayan hari da ƴanbindiga suka kai Makurdi.

    Ko a makonni biyu da suka wuce ma, ƴanbindiga sun kashe aƙalla mutum 25 a wasu hare-hare guda biyu a jihar ta Benue.

  2. Hotuna bayan harin Iran a Isra'ila

    Mun fara ganin hotuna bayan harin da Iran ta kai wa Isra'ila a jiya Asabar.

    Hare-haren Iran ɗin sun ruguza gidaje a yankunan arewaci da kuma tsakiyar Isra'ila, bayan da makaman linzami suka faɗa cikin ƙasar a cikin dare - domin mayar da ramuwa kan hare-hare ta sama da sra'ila ta kai mata.

    Jami'an ba da agajin gaggawa a Isra'ila sun ruwaito mutuwar aƙalla mutum goma, tare da jikkata sama da 100.

    Isra'ila

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Jami'an ceto a wani gini da aka ruguza a birnin Rehovot, da ke tsakiyar Isra'ila
    Isra'ila

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, A safiyar yau a tsakiyar Isra'ila, ɓaraguzai kaɗai ake gani a wasu gine-gine da harin Iran ya lalata
    Isra'ila

    Asalin hoton, EPA

  3. 'Safiya ce mai wahala da kuma baƙin ciki' - Shugaban Isra'ila

    Isaac Herzog

    Asalin hoton, Getty Images

    "Wannan safiya ce mai baƙin ciki da kuma wahala," kamar yadda shugaban Isra'ila Isaac Herzog ya wallafa a shafin X, a daidai lokacin da ƙasar ta wayi gari da hare-haren da Iran ta kai tsakiyar ƙasar da kuma yankuna da ke arewaci.

    Hare-haren Iran "masu muni" sun kashe tare da jikkata "Yahudawa da Larabawa, ƴan Isra'ila da kuma baƙin haure, ciki har da yara da tsofaffi, mata da maza," in ji Herzog.

    Ya ƙara da cewa: "Ina makoki da kuma jajantawa iyalan da suka rasa ƴan uwa. Ina addu'ar samun lafiya ga waɗanda suka jikkata da kuma gano mutanen da suka ɓata. Za mu yi makoki tare. Za mu yi nasara tare."

  4. Houthi sun ce sun haɗa kai da Iran wajen kai wa Isra'ila hari

    Ƴan tawayen Houthi da ke Yemen sun ce sun kaddamar da hare-hare kan yankunan Isra'ila.

    Houthi waɗanda ke samun goyon bayan Iran, sun yi ta kai hari Isra'ila tun bayan fara yaƙin Gaza a watan Oktoban 2023.

    A ɗaya gefe, ita ma Isra'ila ta far wa yankunan Yemen da ke karkashin ikon Houthi.

    "Mun tsara harin da muka kai Isra'ila cikin sa'a 24 da suka wuce ne tare da Iran," kamar yadda wani mai magana da yawun ƴan Houthi ya faɗ a wani jabi a gidan talabijin a yau Lahadi.

  5. Isra'ila ta kai hari kan defo ɗin man Iran

    Tehran

    Asalin hoton, Reuters

    Isra'ila ta ce ta kai hari kan babban defon man fetur na Shahran da ke Iran.

    Lamarin ya janyo ɓarkewar gobara a defo ɗin.

    Sai dai Iran ta ce an samu nasarar hana wutar bazuwa zuwa cikin wasu tankoki.

    Tehran ɗin ta kuma tabbatar da cewa lamarin bai shafi ayyuka a wurin ba, kuma ana ci gaba da aikin raba mai yadda aka saba.

  6. Iran na ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila

    Isra'ila

    Asalin hoton, EPA

    Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila inda ta kai hare-hare a yankin arewaci da kuma tsakiyar ƙasar.

    Aƙalla mutum takwas ne aka tabbatar sun mutu, inda hukumomi suka ce wasu 200 sun jikkata.

    An kashe wasu mata a wata unguwar Larabawa da ke gabashin birnin Haifa.

    An kuma kai hari kan wani gini a garin Bat Yam da ke tsakiyar ƙasar, inda wasu 'yan Isra'ila uku suka mutu.

    Wakilin BBC ya ce hotuna da aka ɗauka a yankin Bat Yam da ke kudancin birnin Tel Aviv - sun nuna ɓarnar da hare-haren suka yi.

    An kuma ji ƙarar abubuwa masu fashewa a birnin Kudus.

    Tun da farko sojojin Isra'ila sun kai hare-hare ta sama kan birnin Tehran, suna masu cewa sun kai hari kan gine-gine masu alaƙa da shirin nukiliyar Iran.

  7. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barkan mu da safiyar Lahadi.

    Ku kasance da mu domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da kuma sauran sassan duniya.