Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/11/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/11/2024

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Annur Muhammad Annur da Isiyaku Muhammed

  1. An kusa fara dakon sakamakon zaɓen Namibia

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Netumbo Nandi-Ndaitwah tana fuskantar ƙalubale daga al'adun siyasa inda maza ne ke sheƙe ayarsu

    Nan bada jimawa ba ake sa ran rufe rumfunan zabe a zaben shugaban kasar Namibiya, wanda ake ganin shi ne mafi zafi tun bayan da ƙasar ta samu ƴancin kai daga ƙasar Afrika ta kudu a 1990.

    Sai dai an samu korafe korafen dogayen layuka da karancin katin zabe a wasu rumfunan zabe.

    Jamiyar SWAPO mai mulki ta tsayar da mace ta farko a matsayin yar takarara shugaban kasa.

    Netumbo Nandi Ndaitwah na fatan maye gurbin Hage Gaingob wanda ya mutu a watan Fabairarun daya gabata bayan ya shafe shekaru tara kan karagar mulki

  2. Mutanen da Trump ya zaɓa a gwamnatinsa sun fara fuskantar barazana

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Wata mai magana da yawun zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump ta ce mutane da ya ba mukamai a gwamnatinsa mai jiran gado sun samu saƙonnin barazana da suka haɗa da na da bama bamai.

    Karoline Laevitt ta ce mutanen da alamarin ya shafa sun haɗa da waɗanda ya ke son ya naɗa a matsayin ministoci.

    Akwai rahotanin da ke cewa mutumin da Donald Trump ya zaɓa a matsayin wanda yake son ya naɗa sakataren harkokin tsaron ƙasar na cikin waɗanda suka fuskanci barazanar.

    Akwai kuma Elise Stefanik wadda Mista Trump ya zaɓa a matsayin jakadar Amurka a majalisar ɗnkin duniya wadda ta ke da gida a New york.

  3. Mai gabatar da ƙara na kotun ICC ya nemi sammacin kama shugaban Myanmar

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Babban mai gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifuka ta duniya , Karim Khan ya bukaci a ba shi sammacin kama shugaban gwamnatin sojin Myanmar.

    Ana zargin Min Aung Hlaing da aikata laifukan cin zarafin biladama akan musulmi yan Rohinja.

    Karim Khan ya ce ''wannan ita ce buƙata ta farko na neman sammacin kama wani babban jami'in gwamnatin Myanmar da ofishina ya gabatar.''

    Mista Khan ya kuma ce akwai karin wasu jami'an gwamnatin ƙasar da za a gabatar mu su da sammaci nan ba da jimawa

    Dubban ƴan Rohinja aka kashe kuma aka tilastawa ɗaruruwa barin gidajensu ko tserewa zuwa ƙasar Bangaladesh.

  4. Magoya bayan Imran Khan sun dakatar da zanga-zanga na wucin gadi

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Magoya bayan tsohon Firaministan Pakistan Imran Khan sun dakatar da zanga-zangar da suke gudanarwa na wani ɗan lokaci, kwana guda bayan da suka yi tattaki a tsakiyar birnin Islamabad.

    Masu zanga-zangar sun sha alwashin ba za su bar babban birnin ƙasar ba har sai an sako Khan.

    Sai dai yayin da suka keta shingen da ke kan hanyarsu ta zuwa dandalin Dimokuradiyya a ranar Talata, ƴansanda sun mayar da su baya inda suka yi amfani da hayaƙi mai sanya hawaye.

    Aƙalla mutane shida haɗane da suka - jami'an tsaro huɗu da fararen hula biyu - suka mutu a arangamar da aka yi a sabuwar zanga-zangar da aka fara ranar Lahadi.

    Jam'iyyar Khan, Pakistan Tehreek-e-Insaf (PTI), ta fada a cikin wata sanarwa a ranar Laraba cewa "an dakatar da zanga-zangar na wani ɗan lokaci" saboda "halayyar gwamnati".

    PTI ta zargi jami'an tsaro da hanƙaɗo wani mutum daga saman tarin kwantenonin dakon kaya a tsakiyar Islamabad, inda ta wallafa bidiyon lokacin da lamarin ya afku a dandalin X.

  5. Gwamnan Kano Abba ya bai wa gwarazan Hikayata kyautar kuɗi

    Gwamnann jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bai wa gwarazan gasar Hikayata guda uku kyautar naira miliyan biyu.

    Usman Bala Muhammad, wanda ya wakilci gwamnan, ya bayyana cewa Gwamna Yusuf ya bayar da kyautar ne domin ƙarfafa gwiwar matan da suka yi fice a gasar.

  6. Hafsat Ganduje ta bai wa gwarazan Hikayata kyautar miliyoyi

    Hafsat Ganduje

    Matar tsohon Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ta yi alƙawarin bai wa mata uku da suka yi nasara a gasar Hikayata ta 2024 kyautar kuɗaɗe.

    A jawabinta, Dr. Hafsat Ganduje ta ce za ta bai wa wadda ta zo ta ɗaya kyautar naira miliyan biyu.

    Ta ce ta biyu za ta samu kyautar naira miliyan ɗaya da rabi, sai kuma ta uku da za ta samu kyautar naira miliyan ɗaya.

  7. Za mu haɗa gwarazan Hikayata da masu shirya fim - Ali Nuhu

    ...

    Shugaban hukumar finafinai ta Najeriya - kuma babban tauraro a Kannywood - Ali Nuhu ya ce burinsu shi ne taimaka wa gwarazan da suka yi nasara a gasar Hikayata.

    Da yake jawabi bayan sanar da gwarzuwar gasar, Ali Nuhu, ya yaba wa BBC Hausa "saboda haɓaka al'adu".

    A cewarsa: "A matsayinmu na hukuma, za mu tabbatar cewa mun nema wa gwarazan wannan gasa hanyar da za su yi aiki tare da masu shirya finafinai."

  8. Hajara Ahmed Hussain ce ta lashe gasar Hikayata 2024

    ...

    Hajara Ahmed Hussain ita ce gwarzuwar gasar Hikayata ta 2024.

    Ta yi wannan nasara ne da labarinta mai suna 'Amon Ƴanci', wanda labari ne kan wata matashiya mai suna Aminatu da ke fafutu.

    Hajara, ta sami lambar yabo da kuma kyautar naira 1,000,000.

    Rayuwa:

    An haifi Hajara Ahmed Hussain a unguwar Kuburu da ke Hadejiya a Jihar Jigawa da ke Najeriya. Ta yi karatun arabiya da boko har zuwa matakin difloma a fannin lissafi, yanzu haka Hajara na da aure da yara.

    Labarin Amon Yanci: Labari ne a kan wata matashiya 'yar makaranta mai suna Aminatu, da take fadi tashi domin sama wa jama'arta 'yanci a kan matsalolin rayuwar da suka musu rubdugu, cikin rashin sa'a kuma sai ta tsinci talatarta a laraba inda ta kare a gidan yari.

    Hajara ta kasance ma'abociyar karance-karance tun lokacin da take sakandire har zuwa lokacin da ta yi aure.

    Takan yi rubutu a takarda da biro amma ba ta samu damar buga su ba har aka fara yi a yanar gizo a shekarar 2015 wanda ita ma ta fara yi a yanar gizo domin isar da sakonni masu yawa ga mutane.

    Ya zuwa yanzu Hajara ta rubuta litattafai kusan 20 baya ga wasu gajerun labarai.

    ...
  9. Labarai da dumi-dumi, Gwamnan Katsina Dikko Radda ya gwangwaje gwaraza da kyautuka

    Gwamnan Katsina Malam Umaru Dikko Radda ya yi alƙawarin bai wa Amra Awwal Mashi kyautar kuɗi da kuma aikin yi.

    Amra 'yar jihar Katsina ce kuma ita ce ta zo matsayi na biyu a gasar Hikayata.

    Wakilin gwamnan a wannan taro ya bayyana cewa gwamnan ya bai wa Amra kyautar kuɗi naira miliyan ɗaya, da kuma ɗaukarta aiki kai-tsaye.

    Kazalika, ya yi wa mutum 12 da ke kan gaba a gasar kyautar naira 250,000 kowacce.

  10. Alhan Islam a kan dandamali

    ...

    Alhan mawaƙiya ce da ta fi shahara a shafukan sada zumunta - yau kuma sai ga ta a taron Hikayata.

    Mawaƙiyar zube ce da yanzu haka take zubo zance a kan dandamali.

  11. Mun yaba da yunƙurin BBC Hausa - Sanata Ali Ndume

    ...

    Ɗanmajalisar dattawa mai wakiltar mazaɓar Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya yaba wa BBC Hausa game da damar da ta bai wa matasa mata a arewacin Najeriya.

    Da yake jawabi, sanatan ya ce BBC Hausa abar alfaharin kowa ce.

  12. Nazifi Asnanic a karo na biyu

    Nazifi Asnanic

    Idan fa ba ku wurin nan ba za ku gane me mahalarta ke ji ba.

    Mawaƙi Nazifi Asnanic ne ya sake dawowa kan dandamali, a wannan karon da waƙarsa mai suna Halitta.

  13. Jakadan Bulgaria a Najeriya ya yi wa BBC Hausa fatan alheri

    ...

    Jakadan ƙasar Bulgaria a Najeriya, Yanko Yordanov, ya yi jawabi, inda ya yaba wa BBC Hausa game da gasar Hikayata.

    "Muna jinjina wa BBC kan yadda suke bai wa matasa dama ta hanyar rubutu," in ji shi.

    Ya ce akwai kyakkyawar alaƙa tsakanin Najeriya da ƙasarsa, da kuma kamanceceniya tsakanin harshen Hausa da nasu.

  14. Labarai da dumi-dumi, Amra Awwal ce ta zo ta biyu

    Amra Awwal

    Amra Awwal Mashi ce ta zo mataki na biyu a gasar Hikayata ta 2024.

    Ta shiga gasar da labarinta mai suna Kura a Rumbu, wanda aka gina kan wata mace da ke yawan hira da maza a shafukan sada zumunta.

    Amra ta samu kyautar kuɗi naira 750,000 da kuma lambar yabo.

    Rayuwar Amrah:

    An haifi Amrah a karamar hukumar Mashi ta jihar Katsina. Ta yi karatun addini da na boko duka a garin Katsina, har zuwa matakin digiri na farko. Amra na da aure da yara biyu. tana sha'awar karance-karance wanda ke ba ta kwarin guiwar yin rubutu. Ta fara rubutu a shekarar 2014. Amrah na sha'awar labaran ban tausayi masu saka kuka.

    Labarin KURA A RUMBU:

    Labari ne a kan wata matar aure wadda ta kasance mai mu'amala da mazan banza da wayarta ta hannu a yanar gizo, a rashin saninta, za ta zama mabudin warwarar matsalar da ta addabi al'ummarta. Gambo Kidinafa ya yi amfani da ita domin cikashe manufarsa, kamar yadda mijinta Habu ɗansanda ma ya yi amfani da ita, Gambo ya shiga hannun hukuma. Da yake ba a fafe gora ranar tafiya, ta yi nadamar da ba ta da amfani a lokacin da rayuwa ta yi mata juyin waina a kasko.

    Bayanan bidiyo, Amra Awwal ce ta zo ta biyu
  15. Labarai da dumi-dumi, Zainab Chubado ta zo ta uku

    ,,,
    Bayanan hoto, Zainab (hagu) ta sami lambar yabo da kyautar Nara dubu ɗari biyar

    Zainab Muhammad CHubado ce ta zo ta uku a gasar Hikayata ta bana.

    Zainab ta shiga gasar ce da labarinta mai suna Tsalle Ɗaya, wanda ta gina shi a kan wata mace mai suna Binta.

    Ta samu kyautar naira 500,000 da kuma lambar yabo.

    ..

    Rayuwar Zainab:

    An haifi Zainab Muhammad Chibado a garin Kafancan na jihar Kaduna.

    Zainab ta yi karatun firamare ne a birnin Kano, sannan ta yi karatun sakandare a garin kafancan.

    Daga nan kuma ta tafi ta yi N.C.E Fedral collage of Education Kano, sannan ta juya B.Ed inda take karantar Education Social Studies. Yanzu haka tana shekarar karshe a jami'ar Ahmadu Bello.

    Labarin Tsalle daya: Labari ne wanda aka gina a kan rayuwar wata baiwar Allah mai suna Binta, wadda tsautsayi da kaddara suka yi sanadin fadawar ta hannun yan garkuwa da mutane, ta sha matukar wahala a hannun su har hakan yai sanadiyar da ta rasa abu mafi mahimmanci a rauwarta, wanda hakan ya zame mata ciwo mafi wahalarwa a cikin tsokar zuciyarta.

    Bayanan bidiyo, Zainab Muhammad Chubado ce ta uku a Gasar Hikayata 2024 ta BBC Hausa
  16. Mawaƙi Hamisu Breaker na gwangwajewa

    ...

    Yanzu haka tauraron mawaƙi Hamisu Breaker ne a kan dandamali.

    Ya fara da waƙe BBC Hausa da waƙarsa mai daɗin gaske.

    Kamar yadda akas saba, ya zarce da shahararrun waƙoƙinsa.

  17. Aikin tantance labarai

    Jagoran tawagar alƙalan gasar Hikayata na bana, Farfesa Salisu Ahmad Yakasai ya yi jawabi.

    Bujimin malamin ya ce sun yi bakin ƙoƙarinsu wajen tantance labaran kafin a samu gwarzuwa ɗaya.

    ..
  18. Nazifi Asnanic na waƙe BBC

    ...

    Shahararren mawaƙi Nazifi Asnanic ya zama babban baƙo na farko da hau kan dandamali, kuma ya yi abin da ya fi ƙwarewa a kai.

    Ya waƙe BBC Hausa da waƙarsa mai suna Ga Tawa.

    Duk wanda ba ya wannan wuri an sha da shi!

    ...
  19. Hikayata 2024: Burin mata uku da labaransu ke kan gaba a bana

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton sama ku kalli bidiyo:

    A yau Laraba za a gudanar da bikin gasar Hikayata - ta gejeru kuma ƙagaggun labarai - a Abuja domin karrama mutum uku da labaransu ke kan gaba.

    Ganin cewa sai a wajen bikin za a sanar da gwarzuwa ɗaya daga cikin uku, mata uku da labaransu ke kan gaba sun bayyana mana burikansu kafin bikin na yau.

    Amra Awwal Mashi: Marubuciyar labarin Kura a Rumbu

    Hajara Ahmad Hussaini: Ita ta rubuta labarin Amon Ƴanci

    Zainab Muhammad Chibado: Marubuciyar labarin Tsalle Ɗaya

  20. Labarai da dumi-dumi, Hikayata 2024: Bikin karrama gwaraza ya ɗauki harama

    Tuni manya da ƙananan baƙi suka cika ɗakin taro a Abuja.

    Wannan ne karo na tara da ake karrama gwarazan gasar.

    Kamar yadda aka yi a shekarar da ta gabata, sai a yau ne za a faɗi gwarzuwar - daga cikin mata uku da ke kan gaba.

    ...
    ...
    ...