Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya 24/12/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 24/12/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Isiyaku Muhammed da Aisha Aliyu Jaafar

  1. An yanke wa mutum biyar zaman gidan yari na wata shida saboda rikicin kwallon ƙafa

    a

    Asalin hoton, VLN NIEWS/ANP/AFP

    Bayanan hoto, A

    Wata Kotu a Netherland ta yanke wa wasu mutum biyar hukunci saboda hannu da suke da shi a tashin hankalin da ya faru gabani da kuma bayan wani wasan ƙwallo tsakanin Maccabi Tel Aviv da Ajax Amsterdam a watan da ya gabata.

    Hukuncin da aka yanke masu ya haɗa da zaman wata shida a gidan yari da kuma aikin taimakon al'umma na tsawon sa'a ɗari.

    Wasu ƙarin waɗanda ake zargi za su bayyana gaban kotu cikin kwanaki masu zuwa.

    Harin da aka kai wa ƴan Isra'ila magoya bayan ƙwallon ƙafa ya janyo zarge-zargen nuna wa Yahudawa ƙyama.

    Sai dai mai gabatar da ƙara ya ce bai kamata a danganta lamarin ga nuna ƙyama ga Yahudawa ba.

    Rikicin da aka yi daidai lokacin da ake fuskantar zaman ɗarɗar kan yaƙin Isra'ila a Gaza, ya faru bayan da wasu magoya bayan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Maccabi suka riƙa rera waƙoƙin adawa da Larabawa tare da ƙona tutar Falasɗinawa.

  2. An ɗage haramcin amfani da Whatsapp a Iran

    A

    Asalin hoton, Reuters

    Iran ta ɗage haramcin da ta ƙaƙaba kan manhajar sada zumunci ta Whatsapp.

    Kamfanin dillancin labarai na ƙasar ya ce wata hukuma ta kaɗa ƙuri'ar cire duk takunkuman da aka ƙaƙaba kan Whatsapp da rumbin sauke manhajoji na Google Play na tsawon fiye da shekara biyu.

    Tsarin sirranta bayanai na manhajar ya sa ya yi wuya ga hukumomin ƙasar su bibiyi hirarrakin mutane kuma hakan ya ci karo da dokokin amfani da intanet masu tsauri da ƙasar ta kafa.

    Amfani da Whatsapp a Iran ya zama jidali saboda da wuya saƙonnin da aka tura ta manhajar su isa ga wanda aka aikawa.

  3. Kwatancin ƙwazon Mo Salah da sauran gwarazan ƴanwasan gaban Premier

  4. Morocco za ta samar da dokar da za ta bai wa mace ikon hana mijinta ƙara aure

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Morocco ta gabatar da shawarwarin samar da wata dokar iyali wadda za ta bai wa mata ƙarin ƙarfin iko a kan riƙon ƴaƴa, da gado da kuma adawa da auren mace fiye da ɗaya.

    Wannan sauyi na zuwa ne bayan shekara 20 masu hanƙoro na fafutikar ganin an tabbatar da ita.

    Haka nan dokar za ta taƙaita auren wuri.

    Dokokin waɗanda suka kai guda 100, na buƙatar amincewar majalisar dokoki da kuma sarkin ƙasar kafin a fara aiki da su.

    Sarki Mohammed ya ce za a yi sauye-sauyen ne bisa tsari na addinin Musulunci domin kare rayuwar iyali.

    A shekarar 2022 ne sarkin na Morocco ya bayar da umarnin fara aiki kan sabbin dokokin.

  5. Yunwa na neman mamaye Sudan - Rahoto

    ...

    Asalin hoton, Mohamed Zakaria/BBC

    Wata hukuma da ke sa ido kan matsalar yunwa a duniya ta ce akwai tsananin yunwa a sassan Sudan da yaƙi ya ɗaiɗaita kuma akwai yiwuwar matsalar za ta bazu cikin watanni masu zuwa.

    Yankunan da matsalar ta fi ƙazanta sun shafi sansanonin ƴan gudun hijira biyu a El Fasher da ke arewacin Darfur da yankuna biyu a jihar kudancin Kordofan.

    Hukumar, wadda Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran hukumomin agaji ke amfani da rahotonta, ta ce fiye da mutum 600,000 ne ke fama da mummunar matsalar yunwa.

    Sannan ƙarin wasu miliyan takwas na cikin haɗarin faɗawa cikin matsalar ta yunwa.

    Kusan rabin al'ummar Sudan na buƙatar agajin abinci. Ƙarancin abincin ya fi muni a sansanoni uku a arewacin Darfur.

    Ma'aikatan agaji a Sudan sun ce rashin abinci mai gina jiki na ƙara bayyana musamman a tsakanin yara.

  6. Zan tabbatar an aiwatar da hukuncin kisa da zarar na koma mulki - Trump

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Zaɓaɓɓen shugaban Amurka, Donald Trump ya ce da zarar an rantsar da shi kan karagar mulki, zai umarci ma'aikatar shari'a ta ƙasar da ta dawo da aiwatar da hukuncin kisa.

    Kalamansa na zuwa ne kwana ɗaya bayan da shugaba Biden ya yi wa wasu fursunoni 37 da ke fuskantar hukuncin kisa rangwame inda ya sassauta hukuncinsu zuwa ɗaurin rai da rai.

    Mista Biden ya ce yana bin zuciyarsa amma Mista Trump ya ce matakin zai jefa ƴanuwan mutanen da aka kashe cikin tashin hankali.

    A zamanin mulkinsa na farko, Trump ya dawo da dokar hukuncin kisa bayan shafe kusan shekara 20 ba a aiwatar da ita.

  7. Zan hukunta duk wanda ya karkatar da kayan noma - Aliyu

    Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu

    Asalin hoton, AHMAD ALIYU

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Aliyu

    Gwaman jihar Sokoto, Ahmad Aliyu ya gargaɗi waɗanda gwamnatin jihar ta bai wa aikin raba kayan aikin noman rani da su kauce wa ayyukan rashin gaskiya da "cin amanar da aka ba su".

    Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ƙaddamar da aikin raba kayan noman rani a garin Wamako na jihar ta Sokoto a ranar Litinin.

    Ya ce "Ina gargaɗin ku da kakkausar murya, kada ku ci amanar da aka ba ku kamar yadda ya faru a lokacin damina.

    "Mun ɗauki matakan tabbatar da cewa an hukunta duk wanda ya yi yunƙurin karkatar da kayan a wannan karo.

    "Ku kasance masu tsoron Alla, ku bari al'umma su amfana da wannan tsari na gwamnati."

    Gwamna Aliyu ya ce gwamnatin Sokoto na ganin cewa babbar hanyar bunƙasa rayuwar al'ummar jihar ita ce ta hanyar bunƙasa ɓangaren noma.

    Ya ce gwamnatinsa za ta raba filayen noman rani hekta 450 ga manoma a yankin Kware, sannan an fara aikin noman rani na Wurno yayin da aka bayar da kwangilar farfaɗo da madatsar ruwa ta Lugu Dam.

    Noma ne babbar sana'ar al'ummar yankin arewacin Najeriya, sai dai a shekarun baya-bayan nan ɓangaren na noma ya samu koma-baya sanadiyyar matsalar tsaro.

    ...

    Asalin hoton, Sokoto State

  8. Gomman mutane guguwar Chido ta kashe ba dubbai ba - Firaministan Faransa

    Faransa

    Asalin hoton, Reuters

    Firaministan Faransa, François Bayrou ya ce mahaukaciyar guguwar Chido da ta kunno kai daga tekun India a ranar 14 ga Disamba a yankin Mayotte, gomman mutane ta kashe ba dubbai ba, kamar yadda wasu suka yi fargaba.

    Bayrou ya shaida wa tashar BFMTV cewa tun a farko yake da amannar cewa adadin da ake faɗa ba gaskiya ba ne.

    Ya tabbatar da cewa waɗanda suka rasu a Mayotte sun kai 35, amma a nasa ɓangaren François-Xavier Bieuville ya ce waɗanda suka rasu sun kai ɗaruruwa, ko ma dubbai kamar yadda ya bayyana a tattauwarsa da kafar France Info.

  9. Muna buƙatar addu'o'inku domin jagoranci nagari - Tinubu

    Tinubu

    Asalin hoton, Tinubu Facebook

    Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya buƙaci ƴan Najeriya su riƙa yi wa shugabanninsu addu'a, inda ya ce su ma suna buƙatar hakan tare da goyon baya domin ƙasar ta ci gaba.

    Tinubu ya bayyana haka ne a saƙonsa na Kirsimeti, inda ya taya al'uumar Najeriya murna, tare da kira gare ga Kiristoci su yi amfani da ranar domin sabunta burinsu na samun ingantacciyar Najeriya.

    Shugaban ya sake jajanta wa waɗanda suka rasu a turmutsutsun Oyo da Anambra da Abuja, inda ya ce shugabanni ma suna buƙatar addu'o'in domin su yi jagoranci nagari.

    Ya kuma yi kira ga ƴan ƙasar su tuna marasa ƙarfi, musamman maƙwabta da ƴan'uwa da abokai da sauran abokan hulɗa.

    "Shugabanni ma suna buƙatar addu'o'i da goyon baya. Idan muka samu goyon bayanku, za mu yi mulki nagari. Najeriya ta kama hanyar inganci domin alamu suna nuna cewa akwai haske a gaba."

    Ya kuma ce za su tabbatar dukkan masu tafiye-tafiye sun je inda za su je lafiya, ta hanyar tabbatar da tsaro da kuma samar da hanyoyin sufuri kyauta.

  10. 'Ƴansanda sun kama mutum fiye da dubu 30 tare da ƙwato makamai a 2024'

    IGP

    Asalin hoton, Nigeria Police Force/Facebook

    Babban sufeto janar na ƴansandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun ya ce jami'an rundunar sun kama waɗanda ake zargi da laifuka daban-daban har mutum 30,313, sannan sun ƙwato makamai 1,984 da alburusai 23,250 a shekarar 2024.

    Shugaban ƴansandan ya bayyana haka ne a taron ganawa manema labarai a ranar Talata, 24 ga watan Disamba a Abuja.

    A wata sanarwa da kakakin rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce sun bayyana nasarar da suka samu ne domin nuna irin shirin fuskantar baɗi da suke yi.

    Shugaban ƴansandan ya yaba da ƙokarin jami'ansa da sadaukarwar da suka yi a shekarar, inda ya ƙara da cewa an samu nasarar ce tare da haɗin gwiwar sauran jami'an tsaro, inda ya ƙara da cewa ana buƙatar hakan domin tabbatar da tsaro mai inganci.

    "Rundunar ƴansandan Najeriya ta samu nasarar daƙile masu aikata laifuka, inda ta samu nasarar kama waɗanda ake zargi da laifuka daban-daban guda 30,313 da ƙwato makamai 1,984 da alburusai 23,250, sannan mun ceci waɗanda aka yi garkuwa da su guda 1,581."

    Ya kuma yi kira ga hafsoshin rundunar su riƙa amfani da kimiyyar zamani domin aikinsu ya ƙara nagarta.

  11. Fafaroma zai ƙaddamar da shekara mai tsarki

    Fafaroma

    Asalin hoton, EPA

    A yau Fafaroma Francis ke shirin ƙaddamar da sabuwar shekara mai tsarki ta mabiya ɗarikar Katolika a faɗin duniya.

    A bisa al'ada, shekarar na zagayowa ne bayan duk shekara 25.

    Fafaroma zai ƙaddamar da bikin a wannan rana ta hanyar buɗe wata ƙofa a fadarsa ta St. Peters Basilica, mai tsarki kafin taron addu'o'in jajibirin Kirsimeti.

    Sama da mabiyan Katolika miliyan 30 ake sa ran su je Rome saboda wannan biki na bana.

    Mahukuntan birnin na ta aikin gyaran tittuna da wuraren tarihi domin tarɓar bakin da za su shigo musu. Mabiyar Katolikan dai sun yi amannar cewa bi ta ƙofar da za a buɗe na kankare zunubai.

  12. 'Ƙungiyoyin ƴantawayen Syria sun haɗe'

    Syria

    Asalin hoton, Getty Images

    Sabuwar gwamnatin Syria ta ce shugabanta, Ahmed al-Shara, ya cimma yarjejeniya da sauran ƙungiyoyin ƴantawayen da ke ƙasar domin haɗewa wuri ɗaya a ƙarƙashin ma'aikatar tsaron ƙasar

    Firaiministan ƙasar, Mohammed al-Bashir ya ce za a yi wa ma'aikatar garambawul domintsofaffin janar-janar na ƙasar da mayakan ƴantawayen su samu damar yin aiki a tare.

    A makon jiya ne gwamnatin, wadda ta Musulunci ce ta naɗa Murhaf Abu Qasra, wanda jigo ne a ƙungiyar HTS da ta kafa gwamnati bayan hamɓarar da gwamnatin Assad a matsayin ministan tsaro.

  13. Ana zanga-zanga a Syria kan ƙona bishiyar Kirsimeti

    Kirsimeti

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni daga Syria na cewa zanga-zanga ta ɓarke a wasu sassa na ƙasar kan ƙona bishiyar Kirsimeti a kusa da birnin Hama.

    Wani bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta ya nuna yadda wasu ƴan bindiga sanye da takunkumi suka bankwa wa bishiyar Kirsimeti wuta, a wani dandali da ke unguwar da Kiristoci ke da rinjaye a garin Suqaylabiyah da ke tsakiyar Syria.

    Sai dai masu kashe gobara sun kashe wutar da ke cin bishiyar.

    Wannan lamarin ne ya ɗaruruwan Kiristoci fitowa zanga-zanga a Damascus da Hama, inda suke kira ga sabuwar gwamnatin ƙasa ta kula da sauran addinai.

  14. Kamfanin American Airlines ya dakatar da zirga-zirga a faɗin Amurka

    Amurka

    Asalin hoton, Getty Images

    A daidai lokacin da ake ta zirga-zirga da tafiye-tafiye domin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara, kamfanin jiragen sama na American Airlines ya dakatar da zirga-zirga a faɗin ƙasat.

    Kamfanin ya ce ya dakatar da zirga-zirgar ne saboda wasu matsaloli na na'ura, wanda suka ce suna ƙoƙarin gyara nan ba da jimawa ba.

    American Airline shi ne kamfanin jirgaen sama mafi girma a yawan fasinjojin da yake safara a faɗin duniya.

  15. Mahara sun kashe mutum 14 a Filato

    Filato

    Asalin hoton, @CalebMutfwang

    Rahotanni sun ce an kashe aƙalla mutum 14, sannan an jikkata wani a wani hari da aka kai a garin Gidan Ado da ke ƙaramar hukumar Riyom da ke jihar Filato.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito daga sakataren watsa labaran ƙungiyar ci gaban mutanen Irigwe wato Irigwe Community Development Association (IDA) Sam Jugo cewa an kashe musu mutum 14, sannan ya ce daga baya sun sanar da dakarun operation safe haven, inda suka kawo musu ɗauki.

    Sai dai kakakin dakarun wanzar da zaman lafiya na jihar bai amsa kiran waya ba, haka shi ma kakakin rundunar ƴansandan jihar.

    Ƙungiyar ta ce an kai harin ne kwana biyu bayan rundunar ƴansandan jihar ta tura jami'anta domin tabbatar da an gudanar da shagulgulan Kirsimeti da Sabuwar Shekara cikin lumana.

  16. Ƴan Houthi sun harba makamai a Isra'ila

    Houthi

    Asalin hoton, EPA

    Ƴan tawayen Houthi da ke Yemen sun harba makamai masu linzami a cikin dare zuwa babban birnin Isra'ila, Tel Aviv.

    Sun harba makaman ne sa'o'i ƙalilan bayan ministan tsaron Isra'ila ya yi alƙawarin ƙara yawan hare-haren da Isra'ila ke kai wa mayaƙan.

    A halin da ake cikin kuma can a birnin Bethlehem, mahaifar Yesu Almasihu, an fara bikin Kirsimeti a yau shekara ta biyu a jere, inda ake bikin ba tare da wata walwala ba.

  17. Kada ku bari a raba kanku - shugaban Jamus

    Frank-Walter Steinmeier

    Asalin hoton, AFP / John Macdougall

    Shugaban ƙasar Jamus, Frank-Walter Steinmeier, ya ce kada ƴan ƙasar su kuskura su bari masu tsattsauran ra'ayi su raba kawunansu -- kalaman da ke zuwa kwanaki huɗu da kai ƙazamin hari a kasuwar cinikin Kirisimeti a Magdeburg.

    Wakilin BBC ya ruwaito Frank-Walter Steinmeier yana cewa harin ya haifar da naƙasu ga shirye-shiryen bikin Kirsimetin bana -- sai dai maƙiya da masu neman tada husuma ba za su yi nasara ba.

    Ana zargin dan gudun hijira daga Saudiyya ne ya kai harin, lamarin da ya tunzura muhawara kan baƙi ƴan ci-rani da kuma tsaron ƙasa.

    A daren Litinni kuma dubban mutane sun shiga zanga-zangar nuna fushinsu da wannan hari a Magdeburg.

  18. Kamfanin Orano na Faransa ya kai ƙarar gwamnatin Nijar kan haƙo Uranium

    Nijar

    Asalin hoton, AFP

    Kamfanin Orano na ƙasar Faransa wanda ke aikin haƙar Uranium a Nijar ya shigar da ƙara a gaban wata kotun shari'ar harkokin kasuwanci.

    Kamfanin ya shigar da ƙarar ne domin ƙalubalantar matakin da gwamnatin ta ɗauka na ƙwace masa kwangilar aikin haƙo Uranium a wurin haƙo ma'adinin na imouraren, wanda yake ɗaya daga cikin mafi girma a Afirka.

    A watan Yunin da ya gabata ne hukumomin mulkin sojan Nijar suka karɓe aikon haƙo ma'adinin daga hannun kamfanin na Orano.

  19. Gwamnan Gombe ya amince da dokar kula da masu buƙata ta musamman

    Gombe

    Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaha ya sa hannu kan ƙudurin dokar kula da masu buƙata ta musamman, wadda ta ƙunshi kafa hukumar masu buƙata ta musamman.

    An yi dokar ce domin samar da daidaito da adalci, tare da tsara hanyoyin da za a taimakawa mutane masu buƙata ta musamman a jihar da kuma tabbatar da cewa ana damawa da su.

    A lokacin bikin sa hannu kan dokar a gidan gwamnatin, Gwamna Inuwa ya sanar da naɗa Ishiyaku Adamu a matsayin shugaban sabuwar hukumar kula da masu buƙata ta musamman da ya kafa.

    Ya ce tun da ya hau kujerar gwamna yake ƙoƙarin kula da masu buƙata ta musamman, inda a cewarsa hakan ya sa ya tun a farko ya naɗa mai taimaka masa na musamman kan harkokinsu.

    Shugaban sabuwar hukumar, Ishiyaku Adamu, ya yi godiya ga gwamnan, tare da yaba masa bisa cika musu alƙawarin da ya yi.

  20. Matar Assad ba ta nemi saki ba - Rasha

    Assad

    Asalin hoton, Getty Images

    Matar hamɓararryen Shugaban Ƙasar Syria, Bashar al-Assad ba ta nemi saki ba, kamar yadda kakakin Kremlin ya bayyana.

    Wasu rahotanni daga kafofin watsa labarai daga Turkiyya ne suka ruwaito cewa Asma al-Assad, wadda asali ƴar Burtaniya ce, ta buƙaci mijinta ya sake ta domin ta bar Rasha, ta koma ƙasarta ta asali.

    Da aka tambaye shi a wani taron manema labarai, Dmitry Peskov ya ce, "labaran ba na gaskiya ba ne."

    Ya kuma ƙaryata rahotannin cewa an ɓoye Assad a Moscow, sannan an ƙwace kadarorinsa.

    Rasha ta kasance ƙawar Syria a zamanin mulkin Assad, inda ta riƙa ba shi gudunmuwar soji a lokacin yaƙin basasa.

    Duk da cewa ƴar asalin ƙasar Burtaniya ce, amma sakataren harkokin wajen Burtaniya ya taɓa faɗa a baya cewa ba za su bari ta dawo ƙasar ba.

    Da yake jawabi a watan jiya a gaban majalisa, David Lammy, ya ce, "zan iya tabbatar muku cewa akwai takunkumi a kanta, kuma ba ma maraba da ita a Burtaniya."

    Ya ƙara da cewa zai yi duk abin da zai iya yi domin tabbatar da cewa babu wani ɗan gidan Assad da ya koma Burtaniya da zama.