Iran ta gargaɗi Birtaniya da Faransa kan duk wani matakin soji a mashigar Hormuz

Asalin hoton, Tasnim news agency
Mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya gargaɗi Birtaniya da Faransa kan duk wani yunƙurin tura sojoji zuwa mashigan Hormuz, yana mai cewa hakan zai haifar da mummunan sakamako.
Gargaɗin nasa ya zo ne bayan wata sanarwar haɗin gwiwa da ƙasashen biyu suka fitar, inda suka bayyana Mashigar Hormuz a matsayin muhimmin hanyar sufuri ga tattalin arzikin duniya, tare da nuna shirinsu na taimakawa wajen tabbatar da tsaron jiragen ruwa da ke bi ta yankin.
A wani saƙo da ya wallafa a dandalin X, Gharibabadi ya ce Hormuz ba wurin nuna ƙarfin soji ba ne ga ƙasashen da ba sa yankin, yana mai jaddada cewa Iran ce ke da alhakin tabbatar da tsaron mashigar tare da sauran ƙasashen da ke gaɓar ruwan yankin.
Ya ƙara da cewa duk wani matakin soji da ƙasashen waje za su ɗauka a yankin zai fuskanci martani, yana mai cewa waɗanda suka haddasa rikici ne za su ɗauki alhakin duk wani sakamako da ka iya biyo baya.






















