Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, Usman Minjibir, A'isha Babangida and Abdullahi Bello Diginza

  1. Rufewa

    Masu bin mu a wannan shafi nan muka kawo ƙarshen labarai da rahotonnin abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu sake dawowa domin ci gaba da kawo muku wasu sabbin labaran.

    A madadin sauran abokan aiki, Abdullahi Bello Diginza ke cewa mu kwana lafiya.

  2. Shugabannin duniya na alhinin rasuwar Navalny

    Shugabannin ƙasashen duniya na ci gaba da alhinin rasuwar jagoran adawar Rasha Alexei Navalvy.

    Mista Navalny ya rasu ne a ɗaya daga cikin gidajen yari mafiya tsaro a ƙasar, inda yake zaman hukuncin da aka yanke masa.

    Shugaban gwamnatin Jamus, Olaf Scholz, ya ce ga alamu jagoran adawar Rashan ya rasa ransa ne saboda jarumtakarsa.

    Firaiministan Birtaniya Rishi Sunak, ya ce Mista Navalny ya kasance na gaba wajen hanƙoron kawo da Dimokradiyya a Rasha.

    Cikin wata sanarwar hadin gwiwa, shugabannin ƙasashen kungiyar tarayyar Turai sun ce sannu a hankali gwamnatin Putin ta kashe Mr Navalny.

    Hukumar kare hakkin ɗan'dam ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta kaɗu da samun labarin mutuwarsa, ta na mai cewa idan har mutum ya mutu a lokacin da ake tsare da shi to ana danganta mutuwar tasa da laifin gwamnatin ƙasar da yake tsaren.

  3. Ƙungiyar AU za ta gudanar da taronta na shekara-shekara a Habasha

    Shugabanin ƙasashen Afirka na ci gaba da isa birnin Addis Ababa, babban birnin ƙasar Habasha, domin fara taron kwana biyu na shekara-shekara, yayin da yaƙi da rashin tsaro da illolin sauyin yanayi ke ci gaba da yi wa nahiyar katutu.

    Batun ilimi na daga cikin manyan batutuwan da taron zai tattauna, yayin da ake sa ran taron zai tattauna batun yaƙin Gaza.

    Saɓanin ikirarin da shugabannin ƙasashen nahyar ke yi na ingantuwar al'amura a yankin, har yanzu nahiyar Afirak na fuskantar barazanar Yunwa da batun sauyin yanayi.

    A lokuta da dama dai ana zargin shugabannin Afirka da rashin daukar matakan da suka dace don magance matsalolin da nahiyar ke fuskanta.

    Kusan shekara biyu bayana taron ƙungiyar na ƙarshe Sudan ta tsunduma cikin mummunan yaƙi.

    Abin jira a gani shi ne ko taron na bana za magance rikicin na Sudan.

    Wani abu kuma da ake ganin taron na bana zai mayar da hankali a kai shi ne batun yaƙin Gaza.

    A watannin baya-bayan nan ƙungiyar ta y ta sukar Isra'ila kan hare-haren da take kai wa Gaza, Kodayake martanin da ƙasashen ke yi game da yaƙin ya bambanta.

  4. MDD za ta taimaka wa Najeriya da kuɗin sayen abinci

    Najeriya da wasu ƙasashe za su amfana da tallafin dala miliyan 50 da hukumar a abinci na Majalisar Dinkin Duniya, WFP, wanda gwamnatin Japan ta ɗauki nauyi.

    Cikin wata sanarwa da hukumar WFP, ta fitar, ta ce ƙasashe 20 ne za su amfana da tallafin, mafi yawancinsu daga nahiyar Afirka da Asiya da yankin Gabas ta tsakiya.

    WFP ta ce kuɗin za su taimaka wa ƙasashen da ke cikin matsin tattalin arziki da waɗanda rikice-rikice da matsalar sauyin yanayi ya yi wa illa.

    Wasu daga cikin ƙasashen da za su amfana da wannan tallafi sun haɗar da Afghanistan da Burkina Faso da Kamaru da DR Kongo da Djibouti da Haiti da Jordan da Laberiya da Mali da Myanmar da Nijar da Najeriya da Falasɗinu da Rwanda da Somaliya da Sudan ta Kudu da Sudan da Uganda da Ukraine da Yemen.

    Hukumar ta WFP ta ce ta yi maraba da matakin ƙasar Japan na bayar da tallafin, musamman a wannan lokaci na ƙarancin tallafi.

    WFP ta ce tallafin zai taimaka wa al'umomin waɗannan ƙasashen da yaƙi da matsalar ɗumamar yanayi da matsin tattalin arziki da ɗaɗaita.

    Japan ta kasance ɗaya daga cikin ƙasashen da ke yawan bai wa hukumar WFP tallafi.

    Hukumar ta ce za a yi amfani da dala miliyan 13.5 na tallafin wajen tallafa wa mutanen da ke cikin tsananin buƙatar abinci mai gina jiki a Afghanistan.

    Haka kuma za a yi amfani da dala miliyan 11 wajen sayen abinci da sauran abubuwan buƙatun rayuwa don tallafa wa al'ummar Falasɗinawa da yaƙi ya ɗaiɗaita.

  5. Sojojin Najeriya sun kashe 'ƴan ta'adda' 254 cikin mako ɗaya.

    Sojojin Najeriya sun ce sun kashe 'ƴan ta'adda 254 tare da kama guda 264 a ayyukan da ta gudanar cikin mako ɗaya a faɗin ƙasar.

    Daraktan yaɗa labaru cibiyar tsaro ta Najeriya, Mano Janar Edward Buba ne ya bayyana haka a wata ganawa da manema labaru a yau Juma'a.

    Ya ce "shirye-shiryen da muke aiwatarwa na yaƙi da ƴan ta'adda da masu tayar da ƙayar baya ya hana masu aikata miyagun laifuka cimma manufofinsu."

    Najeriya dai na fama da matsalolin tsaro a kowane ɓangare na ƙasar.

    Har yanzu ƴan fashin daji na ci gaba da kisa da sace mutane domin neman kuɗin fansa a jihohin Zamfara da wasu makwabtanta.

  6. 'Yansanda sun kama ƙasurgumin mai garkuwa da mutane a Abuja

    Rundunar 'yansandan birnin tarayyar Najeriya, Abuja ta kama wani mutum da tke zargi da zama ƙasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Saidu Abdulƙadir.

    Kwamishin 'yan sandan birnin, CP Benneth Igwe ne ya tabbatar da kamen a lokacin da yake jawabi ga taron manema labarai a birnin rana Juma'a.

    Kamen na zuwa ne yayin da ministan birnin tarayyar Nysom Wike ya sanya ladan nairan miliyan 20 ga duk wanda ya taimaka da bayanan da za su kai ga kama ɓata-garin da suka addabi birnin.

    CP Igwe ya ce an kama mutumin ne bayan da 'yan sanda suka kai samame sansanin masu garkuwa da ke kan iyakan Abuja da jihar Nasarawa ranar Alhamis da daddare.

    Kwamishinan ya ce a lokacin da 'yan bindigar suka ga 'yan sandan sai suka buɗe musu wuta, inda aka yi musayar wuta, kafin daga bisani 'yan sandan su fatattake su.

    ''Bayan arcewar masu garkuwar ne kuma 'yan sanda suka kuɓutar da wasu mutum biyu da suka yi garkuwa da su, tare da lalata sansanin da kuma kama jagoran masu, mai suna Saidu Abdulkadir, wanda dama 'yan sanda sun jima suna nemansa ruwa-a-jallo''.

    “Binciken farko da ofoshinmu ya gudanar ya gano cewa wanda ake zargin, shi ya kitsa harin da aka yi garkuwa tare da kisan hakimin Ketti da ke yankin ƙaramar hukumar birnin Abuja, mista Sunday Zakwai.

  7. Imran Khan ya zaɓi wanda yake son ya zama firaminista

    Tsohon Firaministan Pakistan da ke tsare a gidan yari Imran Khan ya zaɓi Omar Ayub Khan, mutumin da ke wasan ɓuya da 'yan sanda a matsayin wanda yake son zama firaministan ƙasar.

    Omar Ayub Khan za fafata da ɗan takarar jam'iyyar da ke hamayya da mista Khan

    A yanzu haka 'yan sanda na neman Mista Ayub - wanda ɗaya ne daga cikin jagororin jam'iyyar tsohon firaministan - kan zarge-zagen aikata manyan laifuka, wanda kuma hakan bai hana shi tsayawa takara ba.

    Duk da cewa jam'iyyar Mista Khan ta yi ba-zata wajen lashe mafi yawan kujerun - majalisa a zaɓen makon da ya gabata - nasarar da jam'iyyar ta samu ba ta isa jam'iyyar ta kafa gwamnati ba.

    A yanzu haka manyan 'yan takarar da ke neman ɗarewa kujerar firaministan ƙasar, na ƙoƙarin ƙulla ƙawance, inda jam'iyyar Nawaz Sharif ta PML-N ke yunƙurin ƙulla ƙawance da jam'iyyar Bilawal Bhutto Zardari ta PPP.

    Wani babban kusa a jam'iyyar Mista Khan ta PTI, Asad Qaiser ne ya bayyana mista Ayub a matsayin ɗan takarar mista Khan bayan ganawa da shi a gidan yarin.

    'Yan majalisar dokokin za su zaɓi sabon firsaminista, inda Ayub mai shekara 56 zai fafata da Shehbaz Sharif ɗan'uwa ga firaministan na yanzu Nawaz Sharif.

    Mista Ayub ya fara wasan ɓuya da jami'an tsaro ne tun bayan ɓarkewar zanga-zangar da ta biyo bayan kama mista Khan a watan Mayun da ya gabata.

    To sai dai hakan bai hana shi tsaya wa takarar ɗan majalisa ba, nda ya samau nasara a ƙarƙashin jam'iyyar indifenda da ke samun goyon bayan Imran Khan.

    Idan aka zaɓe shi, Mista Ayub ya ce babban abin da zai bai wa fifiko a gwamnatinsa shi ne yin afuwa ga fursunonin siyasa.

    Mista Ayub, jika ne ga Mohamed Ayub Khan, shugaban sojin Pakistan da ya jagoranci ƙasar tsakanin shekarun 1958 zuwa 1969.

  8. Abubuwan da suka kamata ku sani kan kafa ƴansandan jihohi a Najeriya

  9. Shugaban Senegal ya amince da hukuncin haramta ɗaga zaɓen ƙasar

    Shugaban Senegal Macky Sall ya ce zai yi biyayya ga hukuncin kotun tsarin mulkin ƙasar, inda ya ce nan ba da jimawa ba za a fara tattauna lokacin da za a gudanar da zaɓen ƙasar.

    Kotun ta ce matakin ɗage zaɓen shugaban ƙasar da a baya aka shirya gudanarwa cikin wannan wata haramtacce ne.

    Tun bayan ayyana ɗage zaɓen mako biyu da suka gabata, shugaba Sall ke shan matsn lamba game da matakin.

    To sai dai da alama matsin lambar ya haifar da kyakkyawan sakamako.

    Cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar, ta ce Mista Salla zai yi biyayya ga hukuncin kotun tsarin mulkin.

    Sanarwar ta ce shugaban ƙasar, zai tattauna da masu ruwa da tsaki domin saka sabuwar ranar da za a gudanar da zaɓen nan ba da jimawa ba.

    Mista Sall dai bai bayyana ranar gudanar da zaɓen ba, to amma a hukuncin da kotun tsarin mulkin ƙasar ta yanke, ta ce shugaban ƙasar ba zai ci gaba da zama kan karagar mulki ba, bayan ƙarewar wa'adinsa ranar 2 ga watan Afrilu.

    Matakin ɗage zaɓen da mista Salla ya yi ya fuskanci gagarumar adawa, inda masu zanga-zanga suka wasu titunan ƙasar domin nuna adawarsu da matakin.

    Shugabannin addini da ƙungiyar Ecowas sun buƙaci a gudanar da zaɓen ba tare da ɓata lokaci ba.

    Ana kallon Senegal a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da ke da ƙarfin dimokraɗiyya a yankin yammacin Afirka.

  10. Zulum ya ce al'ummar Borno su yi azumi don neman sauƙin rayuwa

    Gwamnatin Jihar Borno ta buƙaci al'ummar jihar su yi azumi a ranar Litinin 19 ga watan Fabrairu, domin neman sauƙin ubangiji dangane da tsadar kayan abinci da fashewar abubuwa a wasu manyan titunan jihar.

    Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi kafar yaɗa labaran jihar.

    “Ina magana da ku a yau cikin tsananin takaici, amma ina da yaƙinin cewa za mu iya magance matsalolin da ke addabar jiharmu'', na damu matuƙa da halin matsin rayuwa da al'ummar jiharmu ke fuskanta, musamman tsadar kayan abinci'', in ji Zulum.

    Gwamnan ya ci gaba da cewa a gwamnatance suna ɗaukar matakan da suka dace don magance matsalar.

    ''Gwamnatinmu na mayar da hankali wajen inganta harkar noma a jiharmu, da nufin haɓaka abincin da muke nomawa domin rage dogaro da abincin tallafi.''

    Zulum ya ce gwamnatin jihar za ta zuba jari a harkokin dabarun noma, domin tallafa wa manoman jihar, wajen inganta harkokinsu.

  11. Ƙungiyar Ƙwadago ta kira zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Najeriya

    Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya, NLC ta ayyana gudanar da gagarumar zanga-zangar kwana biyu a ranakun 27 da 28 ga watan Fabrairu.

    Shugaban ƙungiyar Kwamared, Joe Ajaero, ne ya bayyana haka a shalkwatar ƙungiyar lokacin wani taron gaggawa da ƙungiyar ta kira ranar Juma'a.

    Mista Ajaero ya ce an ɗauki matakin zanga-zangar ne bayan ƙarewar wa'adin kwanaki 14 da ƙungiyar ta bai wa gwamnatin tarayya kan tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.

    Ƙungiyar dai ta bai wa gwamnati wa'adin ne domin da ɓullo da wasu sauye-sauyen da za su magance matsalolin da 'yan ƙasar ke fuskanta sakamakon matsain rayuwa.

  12. Har yanzu na kasa yarda cewa ya mutu - Matar Navalny

    Mai ɗakin jagoran ƴan'adawa na Rasha, Alexi Navalny, wato Yulia Navalnaya ta ce "ba ta san ko a yanzu za ta gaskata labarin mutuwar mijinta ba ko kuma a'a."

    Lokacin da take magana a wani taron manema labarai a birnin Munich, Yulia ta ce ta samu labarin mutuwar mijinta ne kawai ta kafafen yaɗa labaru.

    Ta ce "ba za mu gaskata gwamnatin Putin ba."

    Daga nan sai ta ce matuƙar dai da gaske ne mijin nata ya mutu, to alhakin ya rataya ne a wuyar shugaban Rasha Vladimir Putin.

  13. Akwai yiwuwar gwamnatin Rasha ce ta kashe Navalny - Blinken

    Sakataren harkokin waje na Amurka Antony Blinken ya ce idan dai har da gaske ne batun mutuwar jagoran ƴan adawa na Rasha, Alexi Navalny, to lallai gwamnatin Rasha ce ke da alhaki.

    Blinken ya kuma ce hakan zai ƙara fito da irin ta'annutin da ke cikin gwamnatin ta Vladimir Putin.

    Shi ma shugaban Majalisar Tarayyar Turai, Charles Michel ya ce EU na ganin babu makawa gwamnatin Rasha ce ke da hannu.

    Shugaban ƙungiyar tsaro ta NATO, Jens Stoltenberg ya ce akwai tambayoyi da dama waɗanda dole Rasha ta bayar da amsa.

  14. Saƙo na ƙarshe da Navalny ya wallafa a shafin Instagram

    Madugun adawar Rasha Alexei Navalny ya samu damar aikewa da saƙo ga duniya, ta hannun lauyansa, inda ya aike da saƙo ga matarsa a bikin ranar masoya ta duniya.

    Mista Navalny ya wallafa saƙonsa na ƙarse a shafin Instagram ranar bikin ranar masoya ta duniya da ta gudana ranar 14 ga watan Fabrairu, inda ya aike da saƙon zuwa ga matarsa, Yulia bayan ya wallafa hotunansu tare da ita.

    "A tsakaninmu, akwai birane da dubban kilomitoci, amma duk da haka ina ji a raina cewa kina kusa da ni a kowace daƙiƙa, kuma koyaushe sonki na ƙaruwa a cikin raina'', kamar yadda saƙon ya nuna.

  15. Sudan ta musanta hana kai kayan agaji ga sassan ƙasar

    Ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta musanta cewa majalisar mulkin sojan ƙasar ta hana kai kayan agaji zuwa yankunan da ke ƙarƙashin ikon ƙungiyar RSF, in ji gidan talabijin na ƙasar Sudan TV.

    "Ma'aikatar harkokin wajen kasar ta yi watsi da iƙirarin da wasu kafafen yada labarai suka yi cewa gwamnatin Sudan ta hana kai kayan agaji zuwa wasu yankuna," in ji tashar.

    Tashar ta kara da cewa, ma'aikatar ta ce Majalisar mai cin gashin kanta ta ƙuduri aniyar aiwatar da yarjejeniyar 2023 da RSF don kare fararen hula.

    Hakan na zuwa ne bayan da kafafen yada labarai na cikin gida suka bayar da rahoton cewa hukumomi na hana kungiyoyin agaji jigilar kayayyakin jin kai daga kasar Chadi zuwa yankin Darfur na yammacin Sudan, wanda galibi ke karkashin ikon kungiyar RSF.

    A ranar 11 ga watan Fabrairu, shugaba Abdel Fattah al-Burhan, ya ce isar da kayan agaji ga yankunan da RSF ke riƙe da su, zai faru ne kawai bayan da aka fatattaki kungiyar tare da kawar da su daga garuruwan da ta ke iko da su a halin yanzu, in ji kafofin watsa labarai na sojojin.

    Yunkurin da kasashen duniya ke yi na kawo karshen rikicin da aka kwashe kusan shekara guda ana yi tsakanin sojojin Sudan da ƙungiyar RSF, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane aƙalla 13,000 tare da raba miliyoyi da matsugunansu ya ci tura ya zuwa yanzu.

  16. Amurka za ta gina sansanoni biyar ga sojojin Somaliya

    Amurka ta amince da gina sansanoni biyar ga sojojin Somaliya a wani ɓangare na ƙoƙarin sake gina sojojin ƙasar a daidai lokacin da kasar ke murmurewa daga yaƙin basasa na tsawon shekaru da kuma fada da mayaka, in ji shugaba Hassan Sheikh Mohamud da kafofin yada labaran kasar a jiya.

    "A madadin al'ummar Somalia, ina miƙa godiya ga gwamnatin Amurka kan goyon bayan da take bai wa Somalia baki daya musamman ma sojojin Somalia," in ji shugaban a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin.

    Kamfanin dillancin labaran ƙasar Somaliya ya bayyana cewa shugaba Mohamud da Molly Phee mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka kan harkokin Afirka ne suka sanya hannu kan yarjejeniyar gina sansanonin.

    Sansanonin, waɗanda Mohamud ya ce za su kasance da rukunin kwamandojin sojan Somaliya na Danab, za a gina su ne a manyan birane kamar Mogadishu da Jowhar da Dhusamareb da Kismaayo da kuma Baydhabo.

    Sojojin Amurka ne suka horar da Danab, wanda ake ɗaukarsa a matsayin mafi kwararrun sojojin Somaliya.

  17. Burkina Faso da Mali da Nijar na tattauna kafa ƙungiyar ƙawance

    Ministoci daga Burkina Faso da Mali da Nijar sun gana a Ouagadougou domin tattauna batun kafa ƙungiya a wani ɓangare na ƙarfafa alaƙa tsakaninsu kamar yadda gidan talabijin na Burinabe ya ruwaito.

    "Ga mu a Ouagadougou domin shirya taron ƙoli na shugabannin ƙasashe na ƙawancen ƙasashen yankin Sahel da ake shirin yi nan kusa," in ji ministan Mali, Abdoulaye Maiga lokacin da yake yi wa 'yan jarida bayani bayan ganawa da shugaban mulin soji na Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traore.

    Taron na zuwa ne makonni bayan ƙasashen na Sahel sun sanar da janyewarsu daga ƙungiyar Ecowas inda suke zargin ta da gazawa wajen tallafa musu a yaƙi da 'yan ta;adda da kuma ƙaƙaba musu takunkuman tattalin arziki da suke zargin sun yi haka ne don mutunta ra'ayin ƙasashen waje.

    Ministan tsaron Burkina Faso, Kassoum Coulibaly ya ce taron a Ouagadougou zai ba da kafar ci gaba kan maganar kafa tsare-tsaren ƙawancen.

    Ƙasashen uku sun kafa nasu ƙawancen na ƙasashen Sahel a 2023 inda ya ce ba za su sauya ra'ayi ba kan matakin kafa ƙungiyar.

    • Yadda ficewa daga Ecowas zai shafi Mali da Nijar da Burkina Faso
    • Ƙasashen da Ecowas ta yi nasarar mai da mulkin dimokraɗiyya
  18. Jagoran 'yan hamayya a Rasha, Alexei Navalny ya mutu

    Fitaccen jagoran 'yan hamayya a Rasha, Alexei Navalny ya mutu a wani gidan yari da ke wani yanki mai tsananin sanyi kamar yadda kamfanonin dillancin labarai suka ruwaito abin da hukumar kula da gidan yarin ƙasar ta ce.

    Ana kallonsa a matsayin ɗan adawar da yake yawan sukar Shugaba Vladimir Putin.

    Yana zaman gidan yari na tsawon shekara goma sha tara saboda laifukan da ake ganin ƙulli ne na siyasa.

    A ƙarshen shekarar da ta gabata ne aka mayar da shi gidan yarin da ke yankin Arctic da ake gani a matsayin mafi azabtarwa.

    Hukumar gidan yarin da ke lardin amalo-Nenets ta ce tana bincike kan abin da ya janyo mutuwar tasa, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Tass ya bayyana.

    A tsawon shekaru, Alexey Navalny ya zame wa gwamnatin Rasha, ala ƙaƙai.

    An soma jin sunansa ne a shekara ta 2011 lokacin zanga-zanga a Moscow bayan an tafka maguɗi a zaɓukan majalisun dokokin ƙasar.

    A wajen zanga-zangar jami’an tsaro suka kamashi, kuma tun daga lokacin ya zama madugun ‘yan adawa.

    Yana da dubban magoya baya a shafukan sada zumunta kuma yana yawan bankaɗo abubuwan rashawa, lamarin da ya sa shi tsule idon hukumomi a Rasha.

    A bara ne, aka saka mishi guba, bayan ya ji ba ya jin daɗi a cikin jirgin lokacin yana kan hanyarsa ta zuwa Siberiya. Daga bisani an garzaya da shi zuwa Jamus, inda a nan ƙwararru suka gano cewa akwai gubar Novichok a cikin jininsa.

    A lokacin dai fadar Kremlin ta Rasha ta musanta cewa tana yunƙurin kashe shi, amma kuma bayan kammala jinya a Jamus, yana komawa Moscow a watan Junairun bara sai aka kama shi aka tisa ƙeyarsa zuwa gidan yari.

    An yi zanga-zanga a faɗin ƙasar, bayan an wallafa wani bidiyo da ke zargin shugaba Vladmir Putin da cin hanci da rashawa.

    Alexie Navalny ya mutu ya bar matarsa da ‘ya’ya biyu.

    • Yevgeny Prigozhin: Putin ya miƙa ta'aziyya kan mutuwar shugaban Wagner
    • Putin da Kim: Abokai a lokacin neman makamai
  19. Hukumomi a Chadi sun sa dokar ta ɓaci kan abinci

    Hukumomi a Chadi sun ayyana dokar ta ɓaci kan abinci.

    An yi wannan sanarwar ranar Alhamis - matakin da hukumomin suka ce zai taimaka wa al'ummar Chadi su tantance lokaci na matsala da lokacin gaggawa.

    A cewar dokar, za a samar da taimakon jinƙai na gaggawa kuma tuni aka kafa wani sashe da zai bibiya tare da tantance yadda za a aiwatar da tsarin.

    Shugaban mulkin soji na Chadi, Mahamat Idriss Déby ya ce batun na iya jefa mutane cikin ƙarancin abinci idan har ba a bayar da agaji ba.

    Ministoci ne za su aiwatar da dokar ciki har da ministan kula da sha'anin dabbobi da ministan aikin gona da na albarkatun ruwa da ministan harkokin waje da ministan tsare-tsare da kuma na jin ƙai.

    • Abin da dokar ta-ɓaci kan samar da abinci ke nufi ga talakan Najeriya
    • Ba za mu sa dokar ta baci kan sha'anin tsaro ba a Najeriya - Ministan 'Yan sanda
  20. Kotun koli ta wanke tsohon ministan Naija Delta Godsday Orubebe

    Kotun kolin Najeriya ta kori daukaka karar da gwamnatin tarayya ta yi kan wanke tsohon ministan harkokin Naija Delta, Godsday Orubebe da ta yi bayan tuhumar sa da bayyana kadarar da ba su kenan ba.

    A 2015 ne dai aka gabatar da mr Orubebe a gaban kuliya bisa tuhumar kin bayyana kadarorinsa a takardar bayyana kadorin ma'aikatan gwamnati da ya aike wa da hukumar da da'ar ma'aikata ta kasa lokacin yana minista tsakanin 2007 zuwa 2011.

    A doka dai laifin ya yi karo da sashe na 15 na dokar da'ar ma'aikata ta kasa, ta 2004 sannan kuma abin hukuntawa ne a sashen doka na 23 (2) na dokar.

    Sai dai mista Orubebe bai yarda da aikata wani laifi ba.