Sojojin Isra'ila sun ce Hamas na amfani da asibitoci a Gaza don 'kaddamar da yaki'

Asalin hoton, Reuters
Mun saurari wani jawabi daga mai magana da yawun rundunar tsaro ta sojojin Isra'ila (IDF), Daniel Hagari.
Ya ce Hamas "na kaddamar da yaki daga cikin asibitoci" a Gaza ta hanyar amfani da irin wadannan wurare a matsayin "cibiyoyin ajiye kayan ta'addanci".
Ya yi magana takamaimai a kan asibitin Al Shifa, mafi girma a Zirin Gaza. Ya bayyana wata gagarumar hanyar karkashin kasa mai sarkakiya a kasan ginin wanda ke birnin Gaza, wanda daga wurin ya ce ana iya shirya yadda za a kai hare-hare.
Daniel Hagari ya ce "daruruwan 'yan ta'adda suna tserewa cikin asibitin don buya a can" bayan hare-haren ranar 7 ga watan Oktoba, kuma ya ce Isra'ila na da bayanan sirri da ke nuna cewa "akwai man fetur a asibitocin Gaza, sannan Hamas tana amfani da shi don harkokin ta'addancinta".
Ya kara da cewa Hamas ta yi haka ne saboda, a cewarsa, rundunar sojojin tsaron Isra'ila tana rarrabewa tsakanin "'yan ta'adda da fararen hula" a hare-harenta. Sabanin haka, a cewarsa Hamas tana cutar da 'yan Isra'ila da kuma fararen hulan Gaza.
- Yadda mutane ke dogon layin karɓar gurasa a Gaza
- Iyalan 'yan Isra'ila da Hamas ta kama sun yi zanga-zangar neman sakinsu
















