Nijar ta ga watan Shawwal, Najeriya kuwa sai Litinin za a yi Sallah

Asalin hoton, Sokoto sultanate
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta sanar da ganin watan Shawwal, wanda ya kawo karshen watan azumin Ramadan a kasar.
Tuni dai Shugaba Mohamed Bazoum ya aike da sakon 'Barka da Sallah' ga ilahirin al'ummar kasar a shafinsa na Tuwita, inda ya yi addu'ar zaman lafiya da tsaro da hadin-kan kasar.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Wannan na zuwa bayan Najeriya, makwabciyar Nijar, ta sanar da cewa ba a ga watan ba tare da ayyana Litinin a matsayin ranar Sallah.
Kwamitin ba da shawara kan harkokin addini na Majalisar Sarkin Musulmi tare da hadin gwiwar kwamitin ganin wata na kasa ya ce bai samu wani rahoto daga kwamitoci daban-daban na kasar da ke tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal ba.
Sarkin Musulmin Najeriya dai ya yi wa al'ummar Musulmin Najeriya addu'a da fatan Allah Ya yi musu jagora.
Ya kuma bukace su da su ci gaba da yi wa kasa addu'ar zaman lafiya da ci gaba. Yana yi wa daukacin al'ummar musulmi barka da Sallah.
Haka kuma, wannan na zuwa ne yayin da wasu kasashen Musulmi na duniya da Saudiyya suka sanar da rashin ganin watan a ranar Asabar.






