Ƙayatattun hotunan Afrika: Daga 14 ga watan Janairu zuwa 20 ga wata

An wallafa

Wasu daga cikin zaɓaɓɓun hotunan Afrika da ƴan Afrika daga nahiyar da wasu ƙasashen:

Short presentational grey line
Wasu daga cikin masu neman mafaka bayan ambaliya a Antananarivo babban birnin Madagascar inda suke buga karta a wani wurin motsa jiki a ranar Alhamis.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Wasu daga cikin masu neman mafaka bayan ambaliya a Antananarivo babban birnin Madagascar inda suke buga karta a wani wurin motsa jiki a ranar Alhamis.
Wasu mata kenan ɗauke da madara cikin tukwane a wani wurin bautar Adinnin Hindu a birnin Durban na Afrika Ta Kudu a lokacin bikin Thaipoosam Kavady da ake yi duk shekara

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Wasu mata kenan ɗauke da madara cikin tukwane a wani wurin bautar Adinnin Hindu a birnin Durban na Afrika Ta Kudu a lokacin bikin Thaipoosam Kavady da ake yi duk shekara
A dai ranar, yara ne suke buga ƙwallo a ƙarƙashin turakun wutar lantarki da aka kafa ba bisa ƙa'ida ba a Soweto da ke Afrika Ta Kudu

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, A dai ranar, yara ne suke buga ƙwallo a ƙarƙashin turakun wutar lantarki da aka kafa ba bisa ƙa'ida ba a Soweto da ke Afrika Ta Kudu.
Wani ɗan wasan ƙwallon Zimbabwe kenan yake atisaye a Kamaru a ranar Talata. Ƴan Zimbabwe ɗin daga baya sun ci Guinea, kuma wannan ne karon farko da suka shiga gasar Afcon tun 2006.

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, A dai ranar, yara ne suke buga ƙwallo a ƙarƙashin turakun wutar lantarki da aka kafa ba bisa ƙa'ida ba a Soweto da ke Afrika Ta Kudu
Alƙaliyar wasa Salima Mukansanga ta tabbatar da cewa ba za ta lamunci sashanci ba a yayin wasan da ta yi alƙalanci kuma ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko da ta yi alƙalanci a wasan nahiya

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Alƙaliyar wasa Salima Mukansanga ta tabbatar da cewa ba za ta lamunci sashanci ba a yayin wasan da ta yi alƙalanci kuma ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko da ta yi alƙalanci a wasan nahiya
A ranar Lahadi, wani ɗan ƙasar Mali ne ya yi tsayuwar soja a birnin Limbe na Kamaru kafin ƙasarsa ta soma wasa inda suka yi kunnen doki da Gambiya

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, A ranar Lahadi, wani ɗan ƙasar Mali ne ya yi tsayuwar soja a birnin Limbe na Kamaru kafin ƙasarsa ta soma wasa inda suka yi kunnen doki da Gambiya…
A wani filin wasa na Banjul babban birnin Gambia a ranar Laraba, ana gyarawa da miƙar ma wani jami'in sojan ƙasar da hularsa a yayin rantsar da shugaban ƙasar.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, A wani filin wasa na Banjul babban birnin Gambia a ranar Laraba, ana gyarawa da miƙar ma wani jami'in sojan ƙasar da hularsa a yayin rantsar da shugaban ƙasar.…
An rantsar da Adama Barrow ne a karo na biyu a matsayin shugaban ƙasar da ke Yammacin Afrika bayan lashe zaɓe a watan Disamba.

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, An rantsar da Adama Barrow ne a karo na biyu a matsayin shugaban ƙasar da ke Yammacin Afrika bayan lashe zaɓe a watan Disamba.
A birnin Kumasi na Ghana kuwa a ranar Asabar, Shugaban ƙasar Hungary ne János Áder ya kai ziyara ga Otumfuo Osei Tutu II, wanda shi ne sarkin mutanen Asante.

Asalin hoton, EPA

Bayanan hoto, A birnin Kumasi na Ghana kuwa a ranar Asabar, Shugaban ƙasar Hungary ne János Áder ya kai ziyara ga Otumfuo Osei Tutu II, wanda shi ne sarkin mutanen Asante.
Shugaban ƙasar Burundi Evariste Ndayishimiye ne yake nuna ƙwarewarsa a wajen kaɗa ganga a ranar Laraba - shugaban ya saka kaya da launin tutar ƙasar domin kaɗa shahararriyar gangar ƙasar.

Asalin hoton, @NtareHouse

Bayanan hoto, Shugaban ƙasar Burundi Evariste Ndayishimiye ne yake nuna ƙwarewarsa a wajen kaɗa ganga a ranar Laraba - shugaban ya saka kaya da launin tutar ƙasar domin kaɗa shahararriyar gangar ƙasar.
Ƙananan hafsoshi ne a birnin Benghazi na Libya ke nuna gwanintarsu a ranar Alhamis a yayin yaye hafsoshin.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Ƙananan hafsoshi ne a birnin Benghazi na Libya ke nuna gwanintarsu a ranar Alhamis a yayin yaye hafsoshin.
Ƴan ƙasar Mali kenan a Bamako babban birnin ƙasar inda suke zanga-zanga kan takunkumin da Ecowas da Tarayyar Turai suka saka wa ƙasar bayan sojojin da ke mulkin ƙasar sun ce za su jinkirta zaɓen ƙasar da shekara huɗu.

Asalin hoton, EPA

Bayanan hoto, Ƴan ƙasar Mali kenan a Bamako babban birnin ƙasar inda suke zanga-zanga kan takunkumin da Ecowas da Tarayyar Turai suka saka wa ƙasar bayan sojojin da ke mulkin ƙasar sun ce za su jinkirta zaɓen ƙasar da shekara huɗu.
Makaɗa garaya na daga cikin waɗanda suka shiga faretin a aka yi a birnin Gondar na Habasha a ranar Talata gabannin bikin Timket a Habasha.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Makaɗa garaya na daga cikin waɗanda suka shiga faretin a aka yi a birnin Gondar na Habasha a ranar Talata gabannin bikin Timket a Habasha...
Ana yin bikin ne domin tuna wa da wankan tsarkin da aka yi wa Yesu a Kogin Jordan. A nan mutum biyar ne ake watsa wa tsarkakakken ruwa a ranar Laraba

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Ana yin bikin ne domin tuna wa da wankan tsarkin da aka yi wa Yesu a Kogin Jordan. A nan mutum biyar ne ake watsa wa tsarkakakken ruwa a ranar Laraba...
Asalin bikin ana yinsa ne a Fasilides, wanda tsarkakakken wuri ne a wajen birnin Gondar.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Asalin bikin ana yinsa ne a Fasilides, wanda tsarkakakken wuri ne a wajen birnin Gondar.
A ranar Alhamis, mutane da dama ne suka hau kan titunan Khartoum babban birnin Sudan domin nuna adawarsu da juyin mulkin da aka yi a ƙasar inda suke kira da a bai wa farar hula mulki.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, A ranar Alhamis, mutane da dama ne suka hau kan titunan Khartoum babban birnin Sudan domin nuna adawarsu da juyin mulkin da aka yi a ƙasar inda suke kira da a bai wa farar hula mulki.
Haka kuma a ranar Laraba, an ɗauki hoton wata a lokacin da yake fitowa inda aka ɗauki hoton ta bayan wata hasumiya a birnin Luxor na Masar.

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Haka kuma a ranar Laraba, an ɗauki hoton wata a lokacin da yake fitowa inda aka ɗauki hoton ta bayan wata hasumiya a birnin Luxor na Masar.

Duka waɗannan hotunan suna da haƙƙin mallaka