Afghanistan : Asusun IMF ya dakatar da ba Afghanistan kudi

An wallafa

Asusun bayar da lamuni na duniya, IMF ya ce ba zai bar Afghanistan ta samu tallafinsa ba saboda rashin tabbaci na amincewa da gwamnatin kasar daga kasashen duniya.

Kafin wannan sanarwa kasar na shirin karbar kusan dala miliyan 460 a mako mai zuwa a matsasin wani tallafi na asusun da zai ba wa kasashe domin farfado da tatalin arzikin duniya da ya samu kansa cikin matsala a dalilin annobar korona.

Karbe iko da gwamnatin Afghanistan din da Taliban ta yi kwatsam, ya sa asusun bayar da tallafin na duniya, ya kasance ba shi da zabi da illa shi ma ya hanzarta yanke hukunci.

Wanda kuma daman tuni asusun ke shirin fara sakin makudan kudaden da suka kai kusan rabin tiriliyan na fam domin tallafa wa tattalin arzikin kasashen duniya.

Kudaden da zai bayar Litinin din nan mai zuwa, wanda kuma kusan dukkanin wata kasa da ke cikin gamayyar asusun za ta samu kasonta ciki har da Burtaniya.

Matakin hana bai wa Afghanistan din wannan kaso nata, na nuni ne ga, abin da kakakin asusun ya kira rashin tabbas a game da amincewa da gwamnatin, wanda hakan a takaice ke nufin kasar, karkashin jagorancin masu iko da ita a yanzu, 'yan Taliban ba za ta samu kudin ba, kamar yadda aka shirya yi a da.

Kuma daman kafin matakin na asusun na IMF, wani jami'in gwamnatin shugaba Biden na Amurka ya gaya wa BBC cewa duk wata kadara ko kudi da gwamnatin Afghanistan take da shi a Amurkar ba za a ba Taliban ba.

Wasu daga cikin 'yan majalisar dokokin Amurkar ma sun matsa wa gwamnatin Biden din daman, inda suka rubuta wa sakataren baitul-malin kasar suka bayyana gwamnatin Taliban a matsayin ta 'yan baranda, suka bukaci da kada a bari su samu kudade daga asusun na IMF.

Shi ma Bankin Duniya yana bayar da kudin gudanar da ayyukan raya kasa da yawa a kasar ta Afghanistan, inda ya ba kasar dala bliyan 5 da miliyan 300 tun 2002.

BBC ta nemi ji daga gareshi kan bayar da irin wadannan kudade a halin yanzu, amma ba ta ji daga wurinsa ba har zuwa lokacin wannan rubutu.

Haka ita ma hukumar tsarin nan na aikewa da kudade a tsakanin kasashen duniya na Western Union ta dakatar da aikawa da kudi Afghanistan har zuwa wani lokaci a nan gaba

Asusun IMF dai ya dauki irin wannna mataki a kan wasu gwamnatocin wadanda yawancin kasashe mambobin asusun ba su amince da gwamnatocinsu ba.

Wannan ya faru a watan Afrilu na 2019 inda asusun ya hana Venezuela taba kudadenta na ajiya na ko-ta-kwana, saboda sama da kasashe 50 mambobin asusun ba su amince da da Shugaba Nicolas Maduro a matsayin halartacen jagoran kasar ba.

Hukumar ta IMF haka kuma ta dakatar da biyan Myanmar bayan da sojoji suka yi juyin mulki a kasar.