Ghana za ta sake gina ofishin jakadancin Najeriya da ke Accra

Nigerian Embassy Ghana

Asalin hoton, Dele Momodu Twitter

Bayanan hoto, An kama mutum biyu bisa zargin hannu a rusa ginin
An wallafa

Ministar harkokin wajen Ghana ta ce kasarsa za ta sake gina ofishin jakadancin Najeriya da ke Accra wanda aka rusa.

A makon da ya wuce ne wasu mutane dauke da makamai suka lalata ginin wanda ba a kammalashi ba.

Tuni aka damke mutane biyu bisa zargin wannan aika-aikar.

Ministar harkokin wajen, Shirley Ayorkor Botchwey ta ce gwamnati za ta gaggauta gyara wuraren da aka rusa a ginin.

Ta ce za a kuma bai wa ofishin jakadancin Najeriya cikakkun takardun filin.

Ms Botchwey ta kara da cewa Ghana za ta ci gaba da aiki domin tabbatar da cewa an kare ma'aikatan jakadancin a cikin kasar.

A cewarta gwamnatinsu na tattaunawa da Najeriya domin warware matsalar.

A ranar Litinin, 'yan Najeriya mazauna Ghana sun yi zanga-zanga kan rusa ginin.

Protesters
Protesters