Coronavirus: Haihuwa a jirgi ta kawo tsaikon dawo da 'yan Najeriya daga Dubai

Wannan ne ya tilastawa jirgin koma wa zuwa Dubai saboda matar
An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Jirgin da ya kwaso 'ƴan Najeriya daga Dubai ya koma bayan wata mata ta haihu a cikinsa jim kaɗan da tashinsa zuwa Legas.

Sanarwar da hukumar da ke kula da 'ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje ta fitar, ta ce matar ta haifi namiji a cikin jirgin Emirates da ke ɗauke da 'ƴan Najeriya, minti 30 bayan ya baro Dubai.

Wannan ne ya tilastawa jirgin komawa Dubai, a cewar sanarwar.

Ta kara da cewa, matar tana asibiti yanzu haka ana kula da lafiyarta da ta jaririnta waɗanda ke cikin ƙoshin lafiya.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Sanarwar ta ce an sauya jirgin, kuma yana kan hanya zuwa Legas ɗauke da ƴan Najeriya 265.

A ranar Talata ne ma'aikatar ƙasashen waje ta Najeriya ta ce za ta fara kwashe ƴan kasar da suka maƙale a wasu ƙasashe sakamakon hana tafiye-tafiye saboda annobar korona.

Ta ce za a kwaso tawagar farko ta 'yan Najeriya 265 ne daga Dubai a ranar Laraba, sannan kuma a kwaso mutum 300 daga Landan.