Jihar Sokoto ta ayyana yau Talata ranar hutun sabuwar shekarar Musulunci

Asalin hoton, Ahmed Aliyu/x
Gwamnatin Jihar Sokoto ta ayyana ranar Talata, 16 ga watan Yuni 2026, a matsayin ranar hutu a hukumance domin bikin fara sabuwar shekarar Musulunci 1 ga watan Muharram ta 1448 bayan hijira.
Hakan na cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar domin bai wa al’ummar Musulmi damar gudanar da bukukuwan sabuwar shekarar cikin natsuwa.
Gwamna Ahmed Aliyu ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da wannan dama wajen yin addu’o’i domin samun zaman lafiya, musamman ganin yadda matsalolin tsaro ke addabar wasu sassan jihar da ma kasa baki daya.
Ya bayyana rashin tsaro a matsayin babbar barazana ga ci gaban Najeriya, inda ya jaddada muhimmancin hadin kan kowa wajen shawo kan matsalar.
Gwamnan ya kuma ce gwamnatocin tarayya da jihohi na ci gaba da kokari wajen tallafa wa hukumomin tsaro don yakar ta’addanci da sauran miyagun laifuka.
Gwamna ya kuma yi kira ga Musulmi da su yi nazari a kan rayuwarsu tare da gyara kura-kuran da suka gabata a sabuwar shekarar 1448 AH.
















