Adadin mutanen da suka mutu a Najeriya ya kai 10 - NCDC

Covid-19

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Hukumar dakile yaduwar cutuka a Najeriya ta ce ya zuwa karfe 9:30 na daren ranar Asabar, an samu karin mutum 13 da suka kamu da coronavirus a kasar.

Wannan na nufin adadin mutanen da suka kamu da cutar a kasar ya kai 318 jimilla.

Hukumar ta ce 11 daga cikin karin mutum 13 na Jihar Legas sai 1 a Delta da kuma daya a Kano - jiha ta baya-bayan nan da cutar ta bulla.

A cewar hukumar, cutar ta covid-19 ta bulla a jihohi 19 cikin 36 da ke kasar kuma kawo yanzu, an sallami mutum 70 daga asibiti sai guda 10 da suka riga mu gidan gaskiya.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

  • Lagos- 174
  • FCT- 56
  • Osun- 20
  • Edo- 12
  • Oyo- 11
  • Ogun- 7
  • Bauchi- 6
  • Kaduna- 6
  • Akwa Ibom- 5
  • Katsina-4
  • Delta- 3
  • Enugu- 2
  • Ekiti- 2
  • Rivers-2
  • Kwara- 2
  • Ondo- 2
  • Benue- 1
  • Niger- 1
  • Anambra- 1
  • Kano-1
Karin bayani kan coronavirus
Karin bayani kan coronavirus

Karin labaran da za ku so ku karanta