Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Adadin mutanen da suka mutu a Najeriya ya kai 10 - NCDC
An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1
Hukumar dakile yaduwar cutuka a Najeriya ta ce ya zuwa karfe 9:30 na daren ranar Asabar, an samu karin mutum 13 da suka kamu da coronavirus a kasar.
Wannan na nufin adadin mutanen da suka kamu da cutar a kasar ya kai 318 jimilla.
Hukumar ta ce 11 daga cikin karin mutum 13 na Jihar Legas sai 1 a Delta da kuma daya a Kano - jiha ta baya-bayan nan da cutar ta bulla.
A cewar hukumar, cutar ta covid-19 ta bulla a jihohi 19 cikin 36 da ke kasar kuma kawo yanzu, an sallami mutum 70 daga asibiti sai guda 10 da suka riga mu gidan gaskiya.
- Lagos- 174
- FCT- 56
- Osun- 20
- Edo- 12
- Oyo- 11
- Ogun- 7
- Bauchi- 6
- Kaduna- 6
- Akwa Ibom- 5
- Katsina-4
- Delta- 3
- Enugu- 2
- Ekiti- 2
- Rivers-2
- Kwara- 2
- Ondo- 2
- Benue- 1
- Niger- 1
- Anambra- 1
- Kano-1
Karin labaran da za ku so ku karanta