Coronavirus: Hissene Habre zai bar gidan yari na wata 2

Hissene Habre

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

An bai wa tsohon shugaban kasar Chadi Hissene Habre hutun wata biyu daga gidan yari a Senegal inda ya ke zaman daurin rai-da rai saboda laifin cin zarafin bil adama.

An dai ba shi hutun ne bayan lauyansa ya bukaci hakan saboda raunin da tsohon shugaban na Chadi ke da shi.

Wani alkali ne dai ya bayar da umarnin a ba shi hutun saboda a yanzu haka ana amfani da gidan yarin da Hissene Habre ke zaune wajen killace sabbin wadanda suka kamu da annobar coronavirus a kasar.

An dai yankewa tsohon shugaban na Chadi hukunci ne bayan an same shi da laifin cin zarafin bil adama a 2016, abin da ya sa aka yanke masa hukuncin daurin rai da rai ke nan inda ya ke zaman a Senegal.

An dai same shi da laifukan da suka hadar da fyade da azabtarwa tare da bayar da umarnin kisa a lokacin mulkinsa wanda ya yi a tsakanin shekarar 1982 zuwa 1990.

To sai dai kuma ya musanta zargin da ake masa na cewa ya bayar da umarnin kisan mutane dubu arba'in a lokacin mulkinsa.

Wannan ne dai karon farko da kotun da ke samun goyon bayan kungiyar kasashen Afirka ta yi kokarin hukunta wani shugaba na Afirka a kan laifin cin zarafin bil adama.

Mr Habre dai zai yi wannan hutun nasa na wata biyu ne a gidansa da ke Ouakam, wata gunduma da ke Dakar babban birnin kasar Senegal, sannan daga bisani kuma ya koma gidan yarin idan komai ya lafa.

Hissene Habre shi ne tsohon shugaban kasa na farko a nahiyar Afrika da aka yi wa shari'a a wata kasa.

Sannan ya tsere zuwa Senegal ne bayan da aka hambarar da gwamnatinsa a 1990.

Karin bayani kan coronavirus