Kotu ta dakatar da bincike kan Sarkin Kano

Asalin hoton, BALANCY EMIRATE PHOTOGRAPHY
Wata babbar kotu a jihar Kano ta dakatar da hukumar sauraron kararrakin jama'a da yaki da cin hanci da rashawa daga gayyatar Sarkin Kano kan wani bincike dangane da zargin karkatar da kudin masarauta.
Sarki Muhammadu Sanusi II ya nemi kotu ta dakatar da binciken da hukumar take yi masa ne, wanda ta ba shi wa'adin ranar Litinin da ya gurfana a gabanta.
Sarkin ya shigar da kara ne gaban Mai Shara'a A. Lewis-Allagoa na babbar kotun tarayya da ke Kano, inda ya bukaci kotun ta dakatar da gayyatar har sai ta duba korafin da ya shigar gabanta.
A cikin hukuncin da kotun ta bayar wanda BBC ta gani, Mai Shari Lewis-Allagoa ya amince da bukatar mai shigar da kara wato Sarkin Kano.
Alkalin ya umarci hukumar da shugabanta Muhyi Magaji da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wadanda su ne aka yi kara, da su dakatar da binciken har sai kotu ta yi hukunci kan batun.
Kotun ta yi umarni da a isar wa wadanda aka yi kara umarninta sannan kuma ta dage sauraron batun har zuwa 18 ga watan Maris na 2020.
A ranar Alhamis ne Muhyi Magaji Rimin Gado ya shaida wa BBC cewa tuni suka fada wa lauyoyin mai martaba cewa sarkin ya gurfana gabanta ranar Litinin.
Sarkin Kanon dai na fuskantar tuhume-tuhume daga bangarorin gwmnati daban-daban.
Ko a ranar Alhamis ma majalisar dokokin jihar ta kaddamar da wani binciken a kansa. Sai dai kawo yanzu masarautar Kano ba ta ce komai ba.
Barista Muhyi ya ce sashe na 31 na dokar da ta kafa hukumar ya tanadi duk wanda aka gayyata ya zo da kansa.











