'An soke tashin jirginmu saboda mu Musulmi ne'

Asalin hoton, Reuters
Wasu maza biyu Musulmi 'yan Amurka sun bukaci a gudanar da bincike inda suka bayyana cewa an nuna musu bambancin addini yayin da suke kokarin koma wa gida.
Abderraoof Alkhawaldeh da kuma Issam Abdallah sun yi zargin cewa an soke tashin jirgin da za su bi zuwa birnin Dallas sakamakon ma'aikatan cikin jirgin ba su aminta da zamansu cikin jirgin ba.
Mista Abdallah ya shaida wa manema labarai cewa ''wannan ranar ita ce ranar da aka fi wulakanta ni a duniya.''
Sai dai sanarwar da kamfanin jirgin ya fitar ta bayyana cewa ''akwai daya daga cikin ma'aikatan jirgin da ya koka da kuma wani fasinja'' wanda hakan ya sa aka soke tashin jirgin.
Me ya faru a cikin jirgin?
Mista Alkhawaldeh da kuma Mista Abdallah sun yi zargin ne a wani taron manema labarai da wata kungiyar Musulmai ta Amurka ta shirya, inda suka yada taron kai tsaye a shafin Facebook.
A ranar 14 ga watan Satumba ne mazan biyu suka shirya tafiya zuwa Birmingham da Alabama kafin su wuce gidansu da ke Dallas.
Sun shirya shiga wani jirigin Amurka wanda wani kamfanin jirgi na Mesa Airlines ke rike da harkokin gudanarwar jirgin.
Mazan sun bayyana cewa wurare daban-daban za su je amma da yake sun gane juna a matsayinsu na Musulmai sai suka daga wa juna hannu a cikin jirgi. Wata kila wannan dalili ne ya sa aka fara zargin su.
Mista Abdallah ya bayyana cewa ya je makewayi a cikin jirgin, bayan ya fito sai ya ga daya daga cikin ma'aikatan jirgin labe jikin kofar makewayin.
Lokaci kadan bayan hakan aka yi sanarwar cewa an soke tashin jirgin.
Mista Alkhawaldeh ya bayyana cewa ya ji daya daga cikin ma'aikatan jirgin yana fada wa wani fasinja cewa an soke tashin jirgin saboda tsaro.
Sun bayyana cewa, suna sauka daga cikin jirgin kenan jami'an tsaro suka tafi da su suka bincike su tare da tambayoyi.









